Ana Zargin an Dauki Hayar 'Yan Bindiga, Sun Kashe Dan Takarar PDP a Kaduna

Ana Zargin an Dauki Hayar 'Yan Bindiga, Sun Kashe Dan Takarar PDP a Kaduna

  • Miyagun yan bindiga sun kashe dan takarar kansila a jihar Kaduna tare da kaninsa a hanyarsu ta komawa gida
  • Ana zargin harin ba ya rasa nasaba da siyasa, domin ya na dawowa daga yawon yakin neman zabe ne lamarin ya auku
  • Shugaban karamar hukumar Kauru a jihar ne ya tabbatar da kisan Raymond Timothy da kaninsa James Timothy

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

Jihar Kaduna - Wasu yan bindiga sun kashe dan takarar kansila a mazabar Pari, a karamar hukumar Kauru, a jihar Kaduna Raymond Timothy.

Shugaban karamar hukumar, Barnabas Chawai ne ya tabbatar da kisan, inda ya ce an kashe kansilan tare da kaninsa James Timothy.

Kara karanta wannan

Zaki ya hallaka matashi dan Bauchi a gidan zoo da ke dakin karatu na tsohon shugaban kasa

Kaduna
Kaduna: Yan bindiga sun kashe dan takarar kansila a PDP, Raymond Timothy Hoto: Legit.ng
Asali: Original

A labarin da ya kebanta da Punch zuwa yanzu, an samu tabbacin yan bindiga sun kashe dan takarar kansilan da dan uwansa.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Lamarin ya faru ne suna kan babur a hanyarsu ta dawowa daga yakin neman zabe.

Ana zargin kisan siyasa a Kaduna

Shugaban karamar hukumar Kauru a Kaduna, Barnabas Chawai ya yi zargin kisan dan takarar kansila a yankin, Raymond Timothy ba ya rasa nasaba da siyasa.

Marigayin dan takarar ya bar mace daya da yara uku, kuma matarsa na da juna biyu - ana sa ran za ta haifi na hudu a kwanan nan.

Kisan Kaduna: An nemi daukin yan sanda

An nemi yan sanda su gaggauta daukar mataki kan kisan dan takarar kansila a mazabar Pari da ke karamar hukumar Kauru a Kaduna.

Bayan zargin kisan na da alaka da siyasa, shugaban karamar hukumar, Hon. Chawai ya bukaci jami'an tsaro su sanya matakan dakile irin wannan kisan a gaba.

Kara karanta wannan

Yemi Cardoso ya yi rugu rugu da darajar Naira cikin watanni 12 a Bankin CBN

'Yan bindiga sun sace shugaban NURTW a Kaduna

A baya mun wallafa cewa wasu yan ta'adda sun sace shugaban NURTW a kauyen Kidandan a karamar hukumar Giwa da ke jihar Kaduna karo na biyu.

An sace shugaban ne bayan ya kubuta daga hannun miyagun yan ta'adda inda ya shafe kwanakin 60, amma a wannan jikon, an kwashe shi da yaran makwabtansa guda uku.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano.