Bidiyo: Kashim Shettima Ya Dawo Najeriya daga Kasar Amurka, Zai Gana da Tinubu

Bidiyo: Kashim Shettima Ya Dawo Najeriya daga Kasar Amurka, Zai Gana da Tinubu

  • Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya dawo Najeriya daga taron Majalisar Dinkin Duniya (UNGA) da ya halartar a Amurka
  • Mataimaki na musamman kan harkokin watsa labarai a ofishin mataimakin shugaban kasar, Stanley Nkwocha ya sanar da hakan ranar Lahadi
  • An rahoto cewa Shettima zai gana da Shugaba Bola Tinubu a inda ake gudanar da bubukuwa na murnar cikar Najeriya shekaru 64 da 'yanci

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Abuja - Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya iso birnin Abuja bayan kammala taron Majalisar Dinkin Duniya a birnin New York.

A ranar Lahadi ne Shettima ya dawo Najeriya bayan wakiltar Shugaba Bola Ahmed Tinubu a wajen taron UNGA na 79 da aka kammala a Amurka.

Kara karanta wannan

Yemi Cardoso ya yi rugu rugu da darajar Naira cikin watanni 12 a Bankin CBN

Kashim Shettima ya iso Abuja bayan kammala taron UNGA a Amurka
Abuja: Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya dawo Najeriya daga taron UNGA. Hoto: @stanleynkwocha
Asali: Twitter

Shettima ya dawo Najeriya daga Amurka

Babban mataimaki na musamman kan harkokin yada labarai a ofishin mataimakin shugaban kasa, Stanley Nkwocha ya bayyana haka a shafinsa na X.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sanarwar Nkwocha ta ce:

"A ranar Lahadi ne mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya dawo Abuja bayan samun nasarar wakiltar Shugaba Bola Ahmed Tinubu a wajen taron Majalisar Dinkin Duniya karo na 79 da aka kammala a birnin New York na kasar Amurka.
"Mataimakin shugaban kasar, wanda ya wakilci Shugaba Bola Ahmed Tinubu, GCFR, ya kuma gabatar da bayanin a madadin Najeriya a babban taron."

Shettima zai gana da Shugaba Tinubu

Sanarwar ta kuma ce Shettima ya gudanar da tarurruka da dama da wasu kasashe da kuma sauran abubuwa da suka faru a gefen babban taron.

Bayan isowarsa kasar, sanarwar ta ce Shettima zai:

"Zai hadu da Shugaba Bola Ahmed Tinubu domin gudanar da wasu bukukuwa da aka hada a wani bangare na bikin murnar cikar Najeriya shekaru 64 da samun ‘yancin kai."

Kara karanta wannan

"An yiwa ƙasa addu'a": Tinubu ya haɗu da tsofaffin shugabanni 2 da sarki a masallacin Jumu'a

Tinubu ya fasa zuwa taron UNGA

Tun da fari, mun ruwaito cewa fadar shugaban kasa ta ce Shugaba Bola Tinubu ba zai halarci taron Majalisar Dinkin Duniya karo na 79 za a gudanar a birnin New York ba.

Fadar ta ce Tinubu na so ya mayar da hankali kan al'amuran cikin gida da magance wasu kalubalen da kasar ke fuskanta, musamman bayan ambaliyar ruwa a wasu sassan kasar.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.