Kano, Katsina: Jerin Jihohi 15 da Za a Kwashe Kwanaki 5 Ana Zabga Ruwa da Iska

Kano, Katsina: Jerin Jihohi 15 da Za a Kwashe Kwanaki 5 Ana Zabga Ruwa da Iska

  • Gwamnatin tarayya ta yi hasashen cewa za a zabga mamakon ruwa a jihohi 15 kuma za a iya samun ambaliya daga 24 zuwa 28 ga Satumba
  • Cibiyar ba da sanarwar gaggawa kan ambaliyar ruwa ta kasa (FEWS) ta fitar da hasashen a ranar Talata kamar yadda rahoto ya nuna
  • A yayin da cibiyar ta bukaci masu ruwa da tsaki da su kara sanya ido, FEWS ta kuma lissafa jihohin tare da garuruwan da abin zai shafa

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Abuja - Gwamnatin tarayya ta yi hasashen cewa za a zabga ruwan sama kamar da bakin kwarya a wurare 35 da ke cikin jihohi 15 na kasar nan.

Kara karanta wannan

Baki har kunne: Shugaban APC, Abdullahi Ganduje ya samu manyan nasarori a cikin mako 1

Cibiyar ba da sanarwar gaggawa kan ambaliyar ruwa ta Kasa (FEWS) da ke karkashin ma'aikatar muhalli ta tarayya ce ta fitar da hasashen a ranar Talata.

Gwamnatin tarayya ta yi magana kan hasashen yanayin ruwan sama a jihohin Najeriya
Gwamnatin tarayya ta yi hasashen za a yi ruwan sama kamar da bakin kwarya na kwanaki 5 a jihohi 15. Hoto: Puneet Vikram Singh
Asali: Getty Images

Za a zabga ruwa na kwanaki 5

Hasashen ya nuna cewa, jihohin da aka gano da kewayensu na iya fuskantar mamakon ruwan sama wanda zai iya haifar da ambaliya, inji rahoton The Punch.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Cibiyar FEWS ta yi hasashen cewa za a zabga ruwan ne tare da iska daga ranar Litinin 24 ga watan Satumba zuwa ranar 28 ga Satumbar 2024.

Cibiyar ta bukaci masu ruwa da tsaki da su sanya ido sosai kan yanayin ruwan da za a sheka a kwanakin nan domin daukar matakin gaggawa.

Jihohin da za a zabga ruwan

  1. Delta (Abraka, Agbor, Okpo-Krika, Umukwata, Umugboma, Aboh)
  2. Edo (Ekpoma, Auchi, Irrua, Ilushi, Sabongidda-Ora, Uromi)
  3. Taraba (Gembu)
  4. Kwara (Ilorin)
  5. Kaduna (Kauru)
  6. Kebbi (Ribah)
  7. Zamfara (Majara)
  8. Neja (Mashegu, Kontagora, Lapai, Rijau, Sarkin-Pawa).
  9. Katsina (Bindawa, Daura, Funtua, Bakori)
  10. Nasarawa (Ado, Aso, Mararaba)
  11. Adamawa (Demsa)
  12. Jigawa (Gwaram)
  13. Kogi (Ibaji)
  14. Kano (Kunchi/Gari, Sumaila)
  15. Gombe (Nafada)

Kara karanta wannan

NiMEt: Za a zabga mamakon ruwan sama a Kano, Yobe da wasu jihohin Arewa 14

NiMet: Za a zabga ruwa a Arewa

A wani labarin makamancin wannan, hukumar da ke hasashen yanayi a Najeriya (NiMet) ta bayyana cewa za a iya samun kwarya kwaryan ruwan sama a jihohi 17 na Arewa.

Mun ruwaito hukumar ta sanar da cewa akwai jihohin da ruwan zai yi karbi yayin da wasu jihohin ba zai yi karfi ba amma dai za a iya kwashe kwanaki uku ana tafka shi.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.