APC Ta Roki Tinubu kan Ta’addanci a Zamfara, Ta Zargi Gwamna Dauda Lawal

APC Ta Roki Tinubu kan Ta’addanci a Zamfara, Ta Zargi Gwamna Dauda Lawal

  • Jam'iyyar APC reshen Zamfara ta bukaci Bola Tinubu ya sanya dokar ta baci a jihar saboda matsalar ta'addanci
  • Kakakin jam'iyyar, Yusuf Idris shi ya tabbatar da haka inda ya ce akwai masu neman kawo cikas a yaki da ta'addanci
  • Yusuf ya zargi Gwamna Dauda Lawal karara da cewa bai son yaga an samu nasara a harkar saboda Bello Matawalle

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Zamfara - Jam'iyyar APC a jihar Zamfara ta roki Bola Tinubu alfarma game da ta'addanci a jihar Zamfara.

Jam'iyyar ta bukaci Tinubu ya sanya dokar ta baci domin kawo karshen matsalar rashin tsaro a jihar.

APC ta roki Tinubu sanya dokar ta baci a Zamfara
Jam'iyyar APC a Zamfara ta bukaci Bola Tinubu ya sanya dokar ta baci. Hoto: Dr. Bello Matawalle, Dauda Lawal.
Asali: Facebook

APC ta zargi Dauda Lawal kan ta'addanci

Kara karanta wannan

Rundunar tsaro ta fadi halin da Turji ke ciki bayan kisan Sabubu, ta sha alwashi

Kakakin jam'iyyar a jihar, Yusuf Idris shi ya tabbatar da haka a cikin wata sanarwa da Channels TV ta samu.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Yusuf Idris ya zargi Gwamna Dauda Lawal ta kawo cikas a kokarin yaki da ta'addanci da ake yi a jihar.

Yusuf ya ce gwamnan yana yin haka saboda kiyayyar da ke tsakaninsa da karamin Ministan tsaro, Bello Matawalle.

Ya ce gwamnan yana iya bakin kokarinsa domin ganin ba a samu nasara a yaki da ta'addanci ba saboda siyasa kawai, cewar rahoton Punch.

Yadda ake samun nasara a yaki da ta'addanci

"Wannan yaki da ta'addanci da ake yi a Zamfara karkashin jagorancin Bello Matawalle tabbas ana samun nasara."
"Sai dai abin takaici, Gwamnan Dauda Lawal yana kokarin kawo cikas a nasarorin da ake samu saboda siyasa."
"Yana son yin amfani da rashin tsaro domin siyasarsa ta 2027 kamar yadda a yi a 2023 saboda nasarar yaki da ta'addanci zai iya kawo masa masa cikas."

Kara karanta wannan

Edo 2024: PDP ta fara korafi, dan takara ya fadi makircin da APC ta shirya

- Yusuf Idris

An zargi Dauda Lawal da tsanar Matawalle

Kun ji cewa wata kungiyar matasan jam'iyyar APC soki Gwamna Dauda Lawal game da ta'addanci a jihar Zamfara.

Kungiyar ta ce tsanar da Dauda Lawal ya yi wa karamin Ministan tsaro, Bello Matawalle ta yi yawa.

Hakan na zuwa ne bayan zargin hannu a ta'addanci da ake yi wa Matawalle a yankin Arewa maso Yamma.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.