"Akwai Kulli a Ransa": An Zargi Gwamna da Kawo Cikas ga Matawalle a Yaki da Ta'addanci

"Akwai Kulli a Ransa": An Zargi Gwamna da Kawo Cikas ga Matawalle a Yaki da Ta'addanci

  • Kungiyar matasan jam'iyyar APC soki Gwamna Dauda Lawal game da ta'addanci a jihar Zamfara
  • Kungiyar ta ce tsanar da Dauda Lawal ya yi wa karamin Ministan tsaro, Bello Matawalle ta yi yawa
  • Hakan na zuwa ne bayan zargin hannu a ta'addanci da ake yi wa Matawalle a yankin Arewa maso Yamma

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Zamfara - Matasan jam'iyyar APC sun caccaki Gwamna Dauda Lawal kan ta'addanci a jihar.

Kungiyar Youth Wing Mobilisation Vanguard ta zargi Dauda Lawal da neman rusa kokarin karamin Ministan tsaro, Bello Matawalle.

An caccaki Dauda Lawal kan zargin Matawalle da hannu a ta'addanci
Kungiyar matasan APC ta soki Gwamna Dauda Lawal kan tsanar Bello Matawalle. Hoto: Dr. Bello Matawalle, Dauda Lawal.
Asali: Facebook

Ta'addanci: An soki Dauda Lawal game da Matawalle

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da shugaban kungiyar, Alhaji Ashiru Tukur-Sadauki ya fitar, cewar rahoton Tribune.

Kara karanta wannan

Yunwa na neman kashe shi a Katsina, Kwankwaso ya ceci ran karamin yaro

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Alhaji Ashiru ya ce abin takaici ne yadda Dauda Lawal ya tsani Bello Matawalle da kuma Gwamnatin Tarayya, Vanguard ta ruwaito.

Ya ce halayen Dauda Lawal game da tsanar da ya ke yi wa Tinubu da Matawalle na kawo cikas a yaki da ta'addanci.

An zargi Gwamna da kawo cikas a ta'addanci

"Niyyarsa shi ne kashewa sojoji karfin guiwa a yaki da suke yi da ta'addanci da nasarorin da suke samu."
"Babu dalilin da zai saka Dauda Lawal barin aikinsa na shugaban tsaron jihar, ya kamata a samu hadin kai da shi domin kare rayukan al'umma."
"Sai dai gwamnan ya mayar da hankali wurin bata sunan Bello Matawalle ta kowace hanya."

Wannan na zuwa ne bayan zarge-zargen da ake yi wa karamin Ministan tsaro, Bello Matawalle da cewa yana da hannu a harkar ta'addanci da ake yi musamman a Arewa maso Yamma.

Kara karanta wannan

Borno: Rarara ya fitar da sabuwar waka, ya jajantawa wadanda ambaliya ta shafa

- Alhaji Ashiru Tukur-Sadauki

"Mahaifin Turji mutumin kirki ne" - Sheikh Asada

Mun baku labarin cewa Malamin Musulunci, Sheikh Murtala Bello Asada ya fadi halayen mahaifin Bello Turji.

Sheikh Asada ya ce mahaifin kasurgumin dan ta'addan mai suna Usman Mani ya kasance mutumin kirki ne.

Malamin ya ce bakin cikin Turji ya tilasta Mani komawa Kano kafin ya sake tafiya jihar Jigawa domin rayuwa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.