NECO 2024: Ɗalibai Sun Samu Gagarumar Nasara, Fiye da 60% Sun Ci Turanci da Lissafi

NECO 2024: Ɗalibai Sun Samu Gagarumar Nasara, Fiye da 60% Sun Ci Turanci da Lissafi

  • Hukumar jarrabawar NECO ta fitar da sanarwa a kan sakamakon jarrabawar bana ta gama sakandare a yau Alhamis
  • An ruwaito cewa dalibai da dama sun samu gagarumar nasara inda sama da 60% cikinsu suka yi zalaƙa a Turanci da Lissafi
  • Farfesa Dantani Ibrahim Wushiwushi ne ya bayyana yadda sakamakon ya fito a hedikwatar NECO a birnin Minna

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.

Jihar Niger - Hukumar jarrabawar NECO ta yi karin haske bayan sakin sakamakon jarrabawar na shekarar 2024.

Hukumar NECO ta ce a shekarar 2024, mafi yawan ɗaliban da suka rubuta jarrabawar sun samu Turanci da Lissafi.

Jarrabawar NECO
Dalibai sun yi kokari a jarrabawar NECO. Hoto: Nony and sons
Asali: Facebook

Leadership ta wallafa cewa shugaban NECO, Farfesa Dantani Ibrahim Wushiwushi ne ya fitar da sanarwar a jihar Neja.

Kara karanta wannan

SSCE 2024: Hukumar NECO ta fadi adadin makarantun da suka yi satar amsa

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

NECO: Dalibai 60% sun ci Turanci da Lissafi

Hukumar NECO ta bayyana cewa a jarrabawar shekarar 2024 dalibai kashi 60.55% ne suka ci darusan Turanci da Lissafi.

Rahotanni sun nuna cewa dalibai kashi 60.55% din sun samu darusa biyar da ake buƙata idan aka hada da cin Turanci da Lissafi da suka yi.

Farfesa Dantani Ibrahim Wushishi ya ce dalibai da suka ci darusa biyar ba tare da lura da Turanci ko Lissafi ba sun kai kashi 83.90%.

Satar amsa ta ragu a jarrabawar NECO

Tribune ta wallafa cewa shugaban hukumar ya tabbatar da cewa a wannan karon an samu raguwar satar amsa da kashi 30.1% a kan abin da ya faru a 2023.

Ya kuma tabbatar da cewa za a gayyaci makarantun da aka samu da satar amsa domin yin bayani a hedikwatar hukumar.

Farfesa Dantani Ibrahim Wushiwushi ya yi kira ga dukkan dalibai da suka rubuta jarrabawar a bana da su ziyarci shafin yanar gizon hukumar domin duba sakamakonsu.

Kara karanta wannan

NECO ta fitar da sakamakon jarrabawar 2024, an yi bayanin ka'idojin dubawa

Yadda za a duba sakamakon NECO

A wani rahoton, kun ji cewa wadanda suka zana jarabawar NECO ta 2024 za su iya duba sakamakonsu ta hanyar ziyartar shafin hukumar na yanar gizo.

Daliban da suka zana NECO kuma suke son duba sakamakonsu, za su yi amfani da lambar rajista, lambar sirri da shekarar jarrabawar.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ibrahim Yusuf avatar

Ibrahim Yusuf (Hausa Editor) Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum. ibrahim.yusuf@corp.legit.ng