Yunwa: Wasu Gwamnonin Jihohin Kudu Sun Fitar da Tsarin Wadata Jama'a da Abinci

Yunwa: Wasu Gwamnonin Jihohin Kudu Sun Fitar da Tsarin Wadata Jama'a da Abinci

  • Gwamnoni shida da ke Kudu maso Yamma sun kammala shirya yadda za a wadata mazauna yankin da abinci
  • Sun cimma matsayar ne a jihar Legas bayan an gudanar da muhimman taruka hudu daga watan Yuni zuwa yanzu
  • Daraktan shirin ci gaban Yammacin Najeriya, Seye Oyeleye ya ce za su aiwatar da shirin a kungiyance da kuma daidaiku

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

Jihar Lagos - Gwamnonin Kudu maso Yammacin kasar nan sun sake hallara a jihar Legas inda su ka kammala fitar da matsaya kan magance yunwa a yankin.

A sanarwar da daraktan shirin ci gaban yankin, Seye Oyeleye ya fitar, ya ce sun shirya tsaf kan yadda za a girbe amfanin gona da adana su saboda jama'a.

Kara karanta wannan

Tsadar abinci: Gwamna ya dauki manyan matakai 2, ya ja kunnen yan kasuwa

Abinci
Yankin Kudu maso Yamma na shirin wadata kan shi da abinci Hoto: Aare Oyedele Muteeu
Asali: Facebook

Jaridar Nigerian Tribune ta wallafa cewa a taron da aka gudanar a Legas, karkashin jagorancin gwamna Babajide Sanwo-Olu, an yaba da kokarin gwamnatin tarayya kan wadata kasa da abinci.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Gwamnonin Kudu maso Yamma sun hada kai

Kungiyar gwamnonin Kudu maso Yamma ta umarci kwamishinonin noma a jihohi shida da ke yankin su gaggauta zama domin duba tsarin samar da abinci da aka fitar.

Taron zai biyo ganawar da gwamnonin yankin su ka rika yi tun a watan Yuni, a wani yunkuri na nemo hanyoyin alkinta amfanin gonakin da za a samu.

Jihohin Kudu maso Yamma sun yi shiri

Shirin ci gaban Yamma a Najeriya ya bayyana cewa kowace jiha shida a yankin ta kammala shirya bayanan matakan samun wadatar abinci.

Daraktan shirin, Seye Oyeleye ya bayyana cewa jihohin sun aiko da daftarin shirye-shiryensu, kuma za a mika jawaban ga shugaban kungiyar gwamnonin yankin.

Kara karanta wannan

Kungiyoyin duniya sun taso Tinubu a gaba, za a gudanar da zanga zanga a kasashe

Abinci: Gwamnan Kudu maso Yamma ya dauki mataki

A baya mun ruwaito cewa gwamnan Ogun, Dapo Abiodun ya ce gwamnatinsa ba za ta amince da kara farashin abinci ba bisa ka'ida a jiharsa ba domin ana jin jiki.

Gwamnan ya kuma bayyana dakatar da karbar haraji daga yan kasuwannin da ke jihar, a daidai lokacin da ya ce ana shirin bijiro da tsarin kayyade farashin kayan abinci.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano.