Kano: Matashi Ya Yi Garkuwa da Kaninsa 'Dan Shekara 4, Ya Nemi Fansar Naira Miliyan 10

Kano: Matashi Ya Yi Garkuwa da Kaninsa 'Dan Shekara 4, Ya Nemi Fansar Naira Miliyan 10

  • Rundunar yan sandan jihar Kano ta yi nasarar cafke wani matashi da ya jagoranci sace wani 'dan kanwar mahaifiyarsa
  • Muhammad Nasir Jamilu, dan shekaru 4 ya gamu da sharrin zamani bayan yayansa, Hisbullah Salisu ya sa an dauke shi
  • An sace yaron a gidansu da ke Sharada, aka nemi fansar N10,000,000 kuma tuni aka fara da basu N300,000

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

Jihar Kano - Rundunar yan sandan jihar Kano ta bayyana nasarar cafke wasu matasa uku bisa zargin sace wani Muhammad Nasir Jamilu mai shekaru hudu.

Matasan sun sace Muhammad ne a gidansu da ke Sharada sannan aka kai shi garin Gwarzo, karkashin jagorancin yayansa, Hisbullah Salisu.

Kara karanta wannan

An samu asarar rai bayan gini ya sake rikitowa a Kano

Jihar Kano
An kama matashin da ya yi garkuwa da kaninsa a Kano Hoto: Abdullahi Haruna Kiyawa
Asali: Facebook

A bidiyon da ya wallafa a shafinsa na Facebook, jami'in hulda da jama'a na rundunar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya ce Hisbullah ya samu taimakon mutum biyu wajen satar.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Yan sanda sun kama masu garkuwa da mutum

Jaridar Nigerian Tribune ta wallafa cewa rundunar yan sandan Kano ta kama wasu matasa; Hisbullahi Salisu, Hassan Ali Rabiu da Hassan Aliyu kan zargin satar yaro.

Matasan sun amsa cewa sun dauke yaron ne tare da barazanar kashe shi idan ba a biya fansar N10,000,000 ba, tuni aka fara ba su N300,000.

"An ceto yaro a Kano," Yan sanda

Rundunar yan sandan Kano ta bayyana cewa an ceto yaro mai shekaru hudu mai suna Muhammad da aka sace a Sharada.

Jami'in hulda da jama'a na rundunar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya ce an mika yaron asibitin kwararru na Murtala Muhammad, inda aka tabbatar da lafiyarsa.

Kara karanta wannan

Mazauna Kano sun tashi da takaici, an tsinci jaririya a ƙarkashin tayar mota

Yan sanda sun ceto matashiya

A baya mun ruwaito cewa rundunar yan sandan Kano da hadin gwiwa da yan sandan Kaduna sun yi nasarar cafke masu garkuwa da mutane a dajin Kaduna.

Kakakin rundunar yan sandan Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya ce an sace matashiyar mai shekaru 20 a Zarewa da ke karamar hukumar Rogo a jihar.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano.