NLC Ta Na Son Jiƙawa Tinubu Aiki, Ta Bukaci Rage Kudin Fetur a Jerin Bukatu 4

NLC Ta Na Son Jiƙawa Tinubu Aiki, Ta Bukaci Rage Kudin Fetur a Jerin Bukatu 4

  • Kungiyar kwadago ta yi magana bayan shiga ganawar gaggawa da ta yi a kan kama shugabanta, Kwamared Joe Ajaero
  • Yan kwadago sun fitar da sababbin bukatu hudu ga gwamnatin tarayya ciki har da rage kudin fetur da aka kara a makon jiya
  • A yau ne jami'an DSS suka kama shugaban NLC na kasa, Ajaero yayin da yake kokarin tafiya Birtaniya domin taron kwadago

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.

FCT, Abuja - Kungiyar kwadago ta yanke matsaya bayan ta shiga taron gaggawa a birnin tarayya Abuja.

Yan kwadago sun bayyana sababbin bukatu da suke so gwamnatin tarayya ta cika masu cikin gaggawa.

Yan kwadago
Yan kwadago sun tura bukatu hudu ga Tinubu. Hoto: @NLCHeadquarters|@officialABAT
Asali: Twitter

Legit ta tatttaro bayanan da yan kwadago suka yi ne a cikin wani sako da kungiyar ta wallafa a shafinta na Facebook.

Kara karanta wannan

Bayanai sun fito kan dalilin kama shugaban kwadago da DSS ta yi

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Bukatun yan kwadago 4

  1. Kungiyar kwadago ta bukaci gwamnatin Bola Tinubu ta dawo da kudin man fetur da aka kara a cikin makon da ya wuce.
  2. Yan kwadago sun bukaci jami'an DSS su gaggauta sake shugabansu, Kwamared Joe Ajaero ba tare da wani sharadi ba.
  3. Haka zalika NLC ta bukaci gwamnatin tarayya ta gaggauta tabbatar da fara biyan mafi ƙarancin albashin ma'aikata na N70,000.
  4. A ƙarshe, kungiyar kwadago ta bukaci gwamnatin tarayya ta rage kudin wutar lantarki da aka kara a Najeriya ba bisa ka'ida ba

NLC za ta yi wani taron gaggawa

Kungiyar kwadago ta sanar da cewa a gobe Talata za ta yi taro na musamman a birnin tarayya Abuja da misalin karfe 9:00 na safe.

Ana sa ran cewa a gobe ne kungiyar kwadago za ta fadi matakin da za ta dauka idan gwamnatin tarayya ba ta biya mata bukatunta ba.

Kara karanta wannan

DSS: Kungiyar kwadago ta shiga damuwa kan halin da shugabanta, Ajaero ke ciki

NLC ta koka ka zargin cin zarafi

A wani rahoton, kun ji cewa kungiyar kwadago ta yi Allah wadai da kama shugabanta, Joe Ajaero da jami'an DSS suka yi a birnin tarayya Abuja.

Yan kungiyar NLC sun bayyana cewa cin zarafi da barazana da gwamnatin tarayya ke musu dole a kawo karshensa a Najeriya cikin gaggawa.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ibrahim Yusuf avatar

Ibrahim Yusuf (Hausa Editor) Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum. ibrahim.yusuf@corp.legit.ng