Jihohi 4 Sun Shiga Matsala, Tinubu Ya ba Su Wa'adin Kwanaki 5 kan Kafa 'Yan Sandan Jiha

Jihohi 4 Sun Shiga Matsala, Tinubu Ya ba Su Wa'adin Kwanaki 5 kan Kafa 'Yan Sandan Jiha

  • Yayin da aka shirye-shiryen kirkirar yan sandan jihohi, an ba jihohi hudu wa'adin kwanaki biyar domin kawo rahotonsu kan lamarin
  • Jihohin da ake zance sun hada da Adamawa da Kebbi da Sokoto da kuma jihar Kwara sannan da birnin Tarayyar Najeriya watau Abuja
  • Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da mukaddashin gwamnan Oyo, Bayo Lawal ya fitar a yau Laraba 4 ga watan Satumbar 2024

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

FCT, Abuja - Kwamitin tattalin arziki (NEC) ya yi zama a birnin Tarayya Abuja kan lamuran da suka shafi ƙasar a Aso Rock.

Yayin taron kwamitin, an ba jihohin Najeriya hudu wa'adin kwanaki biyar kan kawo rahoto game da kafa yan sandan jihohi.

Kara karanta wannan

"Babu wanda ya tsira": Miyagu sun fasa ofishin gwamnan APC, sun yashe kaya

Tinubu ya umarci wasu jihohi kan kirkirar yan sandan jiha
Gwamnatin Tinubu ta ba jihohi umarni na rahotonsu kan yan sandan jiha. Hoto: @DOlusegun.
Asali: Facebook

Yan sandan jiha: Tinubu ya ba jihohi wa'adi

An gudanar da taron ne a Abuja wanda mataimakin shugaban kasa, Sanata Kashim Shettima ya jagoranta, cewar rahoton TheCable.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Jihohin da aka ba wa'adin sun hada da Kwara da Adamawa da Kebbi da Sokoto da kuma birnin Abuja, Daily Post ta ruwaito.

Kwamitin ya bukaci jihohin su tabbatar sun kawo rahotonsu zuwa 9 ga watan Satumbar 2024 kan ƙirƙirar yan sandan jihohi.

Za a dauki mataki kan jihohin 4

Mukaddashin gwamnan jihar Oyo, Bayo Lawal shi ya tabbatar da haka bayan kammala taron NEC a yau Laraba.

Lawal ya ce kwamitin zai dauki tsattsauran mataki kan jihohin idan ba su kawo rahoton zuwa 9 ga watan Satumbar 2024 ba.

"A yau ne duka jihohin ake tsammanin su mika rahoto kan kirkirar yan sandan jiha saboda kwamitin ya yi dub a kai, amma an samu jihohi hudu da ba su cika ka'idar ban"

Kara karanta wannan

Mataimakin Shugaban kasa ya shiga taron NEC da manyan attajirai 2, bayanai sun fito

- Bayo Lawal

Egbetokun ya ki amincewa da yan sandan jihohi

Kun ji cewa Sufeto Janar na ‘yan sanda, Kayode Egbetokun ya bayyana matsayar rundunar ‘yan sandan Najeriya kan shirin kirkiro da ‘yan sandan jihohi.

A wani taron tattaunawa na yini daya kan lamarin a Abuja a Afrilun 2024, IGP Egbetokun ya ce Najeriya ba ta shirya amfani da ‘yan sandan jihohi ba.

Sufetan 'yan sandan ya bayyana cewa kirkirar ‘yan sandan jihohi zai haifar da rikicin kabilanci, wanda zai kai ga rashin jituwa a jihohin.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.