Rahoton UNICEF: Gwamna a Arewa Zai Binciki Badakalar Sayar da Abincin Jarirai

Rahoton UNICEF: Gwamna a Arewa Zai Binciki Badakalar Sayar da Abincin Jarirai

  • Gwamnatin jihar Sokoto ta ce za ta gudanar da cikakken bincike kan zargin karkatar da abincin jarirai da wasu ma'aikata suka yi
  • Hukumar UNICEF ce ta yi ikirarin cewa wasu ma'aikata sun sace tare da sayar da abincin jarirai da aka rabawa cibiyoyin kiwon lafiya
  • Kwamishiniyar lafiya ta jihar, Asabe Balarabe ta bayyana cewa gwamnati ba ta da masaniya kan hakan har sai da UNICEF ta yi magana

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Sokoto - Gwamnatin jihar Sokoto ta ce za ta binciki zargin da asusun kula da kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF) ya yi.

UNICEF ya yi zargin cewa an sace tare da sayar da abincin jarirai mai gina jiki da aka baiwa jihar domin inganta lafiyar yara masu fama da tamowa.

Kara karanta wannan

Digiri dan Kwatano: Gwamnati ta lissafa jami'o'in Benin, Togo da ta amince da su

Gwamnatin Sokoto ta yi magana kan zargin karkatar da abincin jarirai a jihar
Gwamnatin Sokoto za ta binciki zargin UNICEF na an karkatar da abincin jarirai. Hoto: @Ahmedaliyuskt
Asali: Facebook

"An sace abincin jarirai" - UNICEF

A ranar Laraba ne jaridar Premium Times ta ruwaito cewa UNICEF ya bankado badakalar karkatar da abincin jarirai da ta rabawa jihar Sokoto.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Shugaban UNICEF na Sokoto, Kebbi da Zamfara, Michael Juma ne ya bayyana hakan a wani taron masu tsare-tsare na bayan wata uku da suke gudanarwa a Sokoto.

Ya ce wasu ma'aikata ne suka hada baki da 'yan kasuwa suka karkatar tare da sayar da abincin jariran da aka rabawa cibiyoyin kiwon lafiya daban daban a fadin jihar.

Gwamnati ta dauki mataki

Kwamishiniyar lafiya ta Sokoto, Asabe Balarabe, ta shaida wa Daily Trust cewa gwamnatin jihar ba ta da masaniya kan lamarin har sai da UNICEF ta fito da shi.

Asabe Balarabe ta ce:

“Mun fito daga taro kenan kan wannan batu. Ba za mu taba kyale maganar haka ba, dole ne mu yi bincike kuma mu hukunta masu hannu."

Kara karanta wannan

Garkuwa da Mutane: Likitoci sun tafi yajin aiki saboda garkuwa da wata likita tun 2023

Ta ba jama’a tabbacin cewa gwamnatin jihar ta jajirce wajen ganin ta magance matsalar rashin abinci mai gina jiki ga jarirai, kuma za ta dauki matakin da ya dace kan barayin.

An gano badakalar ruwa a Kano

A wani labarin, mun ruwaito cewa hukumar yaki da rashawa ta jihar Kano, PCACC ta sake bankado wata dakalar kimanin N660m ta kwangilar ruwa da aka bayar.

An ce hukumar ta fara bin diddigin kudin da aka ware domin samar da ruwa a jihar wanda ake zargin an karkatar da kudin ba tare da aiwatar da kwangilar ba.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.