Akalin Alkalan Najeriya Ya Bar Aiki a Gwamnati, Bayanai Sun Fito

Akalin Alkalan Najeriya Ya Bar Aiki a Gwamnati, Bayanai Sun Fito

  • Babban alkalin Najeriya (CJN) Mai shari'a Olukayode Ariwoola ya yo ritaya daga aiki bayan cika shekara 70 a duniya kamar yadda doka ta tanada
  • Mai shari'a Ariwoola ya zama alkalin alkalan Najeriya ne a watan Yuni, 2022 bayan magabacinsa, Tanko Muhammad ya yi murabus
  • Ana raɗe-raɗin dai shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu na shirin ɗauko shugaban alkalan jihar Legas, Mai shari'a Kudirat Kekere-Ekun ta maye gurbin CJN

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

FCT Abuja - Alkalin Alƙalan Najeriya (CJN) na 22, Mai Shari'a Olukayode Ariwoola ya yi ritaya daga aiki bayan cika shekaru 70 kamar yadda doka ta tanada.

An haifi Mai shari’a Ariwoola a ranar 22 ga Agusta, 1954, ma'ana dai a yau Alhamis yake cika shekaru 70 a duniya.

Kara karanta wannan

Najeriya ta yi rashi, tsohon shugaban ICPC ta ƙasa ya riga mu gidan gaskiya

Mai shari'a Olukayode Ariwoola
Akalin Alkalan Najeriya, Mai shari’a Ariwoola ya yi ritaya Hoto: Olukayode Ariwoola
Asali: Twitter

Jaridar Vanguard ta tattaro cewa ajiye aikin Alkalin Alƙalai na 22 a tarihi ya kawo ƙarshen dogon lokacin da Ariwoola ya shafe yana yi wa ɓangaren shari'a hidima.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Taƙaitaccen bayani kan CJN mai ritaya

A ranar 22 ga watan Nuwamban, 2011, Mai Shari'a Ariwoola ya zama ɗaya daga cikin alkalan da ke zama a kotun ƙolin Najeriya.

Daga bisani kuma ya zama babban alkalin Najeiriya (CJN) a ranar 27 ga watan Yuni, 2022, bayan murabus din wanda ya gabace shi, Mai Shari'a Tanko Muhammad.

Majalisar dattawan Najeriya ta tabbatar da nadinsa a matsayin CJN a ranar 21 ga Satumba, 2022, kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

Tun lokacin da aka fara surutu kan batun ajiye aikin CJN a watan Agusta, alamu sun nuna da yiwuwar Mai Shari'a Kudirat Kekere-Ekun ta zama magajinsa.

Kara karanta wannan

Ministan Tinubu ya faɗi gaskiya kan jita jitar yana shirin sauya sheƙa

Ana raɗe-raɗin dai shugabar alƙalan ta jihar Legas, Mai Shari'a Kudirat na iya zama wacce za a naɗa ta zama sabuwar shugabar alkalan Najeriya.

Gwamnati ta ji koken ƴan Najeriya

A wani rahoton kuma gwamnatin tarayya ta bayyana cewa zanga-zangar da aka yi ta ƙara tunatar da ita bukatar ta riƙa sauraron koken jama'a.

Ministan kasafin kuɗi da tsare-tsaren kasa ya ce a yanzu gwamnati na zama ta saurari koken ƴan Najeriya fiye da a baya.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262