Jerin Mutum 22 Da Suka Hau Kujerar Alkalin Alkalai Na Kasa Tun Zamanin Mulkin Mallaka

Jerin Mutum 22 Da Suka Hau Kujerar Alkalin Alkalai Na Kasa Tun Zamanin Mulkin Mallaka

  • Mun kawo jerin duk wanda suka taba rike mukamin Alkalin Alkalai a Najeriya
  • Adetokunbo Ademola shi ne ya fi kowa dade wa a ofis, ya kusa shekara 15 a kujerar
  • A jerin akwai irinsu Taslim Olawale Elias wanda ya yi Ministan shari’a na kasa

Nigeria - Burin duk wani babban Alkali ya zama Alkalin Alkalai na kasa. Alkalin Alkalai wanda ak fi sani da CJN shi ne shugaban bangaren shari’a na kasa.

Shugaban kasa yana zaben babban Alkalin kotun koli a matsayin shugaban Alkalai bisa shawarar NJC. Dole majalisar dattawa ta tantance shugaban Alkalan.

Sannan sai da sa hannun mafi yawan ‘yan majalisa dagoyon bayan majalisar shari’a NJC ne za a iya sauke CJN, ko kuma idan har ya cika shekara 70 a Duniya.

A halin yanzu Mai shari’a Ariwoola ne Shugaba Buhari ya rantsar yau kan wannan kujera.

Kara karanta wannan

Da Duminsa: Buhari ya Rantsar da Jastis Ariwoola Matsayin Alkalin Alkalan Najeriya

Kafinsa an Tanko Mohammed, da Walter Nkanu Onnoghen.

Tanko, Onnoghen, da Uwais da sauran Alkalai 15 da suka hau kujerar Alkalin Alkalai na kasa
Aloma Maryam Mukhtar da Goodluck Jonathan www.thecable.ng

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

Walter Onnoghen ya yi murabus, Tanko ma Haka

Daga baya aka tursasa wa Walter Onnoghen ya ajiye mukaminsa saboda wasu zargi da ke kansa.

Mahmud Mohammed, Dahiru Mustafa, Aloysius Katsina-Alu, Idris Kutigi, Salihu Belgore, Lawal Uwais da Mohammed Bello sun rike kujerar na shekaru 27.

A shekarar 2012 aka samu macen da ta zama CJN. Shugaban kasa na wancan lokaci, Goodluck Jonathan ya nada Aloma Maryam Mukhtar, ta sauka a 2014.

Adetokunbo Ademola, Mohammed Bello, da Muhammad Lawal Uwais sune su ka fi dade wa a ofis. Kafin Ademola, Birtaniyawa ne suka yi ta rike kujerar CJN.

Legit.ng Hausa ta tattaro ‘yan kasa da suka taba zama shugabannin Alkalai a tarihin Najeriya. Mun tsakuro wasu daga cikin bayanan ne daga shafin Wikepedia.

Kara karanta wannan

An Zo Wurin: Matakai 3 Kacal Da Suka Rage ASUU Ta Janye Daga Yajin Aiki

Mulkin Mallaka

1. Sir Edwin Speed, 1914–1918

2. Sir Ralph Combe, 1918–1929

3. Donald Kingdon, 1929–1946

4. Sir John Verity, 1946–1954

5. Sir Stafford Sutton, 1955–1958

Zamanin mulkin Soja

6. Sir Adetokunbo Ademola, 1958–1972

7. Taslim Olawale Elias, 1972–1975

8. Sir Darnley Arthur Alexander, 1975–1979

9. Atanda Fatai Williams, 1979–1983

10. George Sodeinde Sowemimo, 1983–1985

11. Ayo Gabriel Irikefe, 1985–1987

12. Mohammed Bello, 1987–1995

Bayan Mulkin Soja

13. Muhammad Lawal Uwais, 1995–2006

14. Salihu Moddibo Alfa Belgore, 2006–2007

15. Idris Legbo Kutigi, 2007–2009

16. Aloysius Iyorgyer Katsina-Alu, 2009–2011

17. Dahiru Musdapher, 2011–2012

18. Aloma Mariam Mukhtar, 2012–2014

19. Mahmud Mohammed, 2014–2016

20. Walter Samuel Nkanu Onnoghen, 2017–2019

21. Ibrahim Tanko Muhammad, 2019–2022

22. Olukayode Ariwoola, 2022-

Asali: Legit.ng

Online view pixel