An Zargi Gwamnatin Shugaba Tinubu da Satar Dabarar Tattalin Arziki a Wajen Atiku

An Zargi Gwamnatin Shugaba Tinubu da Satar Dabarar Tattalin Arziki a Wajen Atiku

  • Ministan kudi da tattalin arziki ya nuna za a yafewa wasu kamfanoni haraji idan suka dauki ma’aikata da yawa
  • Magoya bayan Atiku Abubakar sun fara cika-baki, su na cewa wajen ‘dan takaran na PDP aka sato wannan tsari
  • Amma an gano cewa dama can Bola Tinubu yana da wannan ra’ayi, tunaninsu ya zo daidai na Alhaji Atiku ne

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

M. Malumfashi ya shafe shekaru ya na kawo labaran Hausa musamman na siyasa, addini, tarihi, wasanni da al’ada

Abuja – Ministan kudi da tattalin arzikin Najeriya, Mista Wale Edun ya na ta kokarin ganin ya farfado da tattalin arzikin kasar nan.

A yunkurin ministan ne ya bayyana cewa gwamnatin tarayya ta na tunanin yafe karbar haraji daga hannun wasu kamfanoni.

Atiku Tinubu
An ce Shugaba Bola Tinubu ya dauko tsarin Atiku Abubakar Hoto: @Dolusegun
Asali: Twitter

Tinubu zai kawo tsarin afuwar haraji

Kamfanonin da za a yi wa afuwar harajin su ne wadanda su ka dauki karin ma’aikata, Nairametrics ta kawo wannan rahoto.

Kara karanta wannan

Ana cikin badakalar kwangila, Gwamna Abba Gida Gida ya rikice da ayyuka a Kano

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Gwamnatin Bola Ahmed Tinubu ta na kuma duba yiwuwar yafe karbar harajin shigo da wasu kayayyaki domin magance tsada a kasar.

Ministan kudin ya amince cewa an shiga matsin lamba saboda Naira ta rage daraja a yau.

"Idan ka dauki Karin ma’aikata, za a yi maka afuwa da biyan haraji. Saboda haka dabaru ne da shugaban kasa zai sa hannu a kansu."

- Wale Edun

An ce Tinubu ya saci dabarun Atiku

Da jin wannan sanarwa sai ‘yan adawa suka fara murna, su na ikirarin gwamnatin Tinubu ta sato dabarar ne wajen Atiku Abubakar.

“Sun dauko wata dabarar daga Atiku, kuma kamar sauran, ba za su aiwatar da kyau ba, sai su fito suna cewa ‘ko Atiku haka zai yi’

Nan take wasu suka maidawa @chosensomto amsa a shafin Twitter, su ka ankarar da shi cewa ba satar wannan tsari aka yi.

Kara karanta wannan

An yi korafin yadda Tinubu ya 'hana' Kashim Shettima rantsar da Shugabar Alkalai

Legit Hausa ta ci karo da wani bidiyo da Chibuzo Mikel ya wallafa a dandalin, a nan aka ji Bola Tinubu yana irin wannan magana.

Da gaske Tinubu ya ari dabarar Atiku?

A wajen wani taro lokacin yakin zaben 2023, Tinubu ya shaidawa duniya yana da wannan tunani a ran shi idan ya karbi mulki.

Shi Atiku ya fadi manufar yin hakan, ‘dan takaran na APC a lokacin ya ki fito da dabarar a fili saboda gudun a saci fikirarsa.

Malami ya shako kuren Bola Tinubu

Ana da labari a hudubar Dr. Bashir Aliyu Umar bayan zanga-zanga, ya ce tun farko gwamnati tayi kuskure a harkar tattalin arziki.

Zanga-zangar da aka yi ta zama hanyar ta’adi maimakon nuna adawa da manufofin Bola Tinubu, dama can an yi gargadin irin hakan.

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng