Kwamishinan Ganduje Ya Gaskata Dan Bello, Ya Tabbatar da Badakalar Murtala Garo

Kwamishinan Ganduje Ya Gaskata Dan Bello, Ya Tabbatar da Badakalar Murtala Garo

  • Tsohon kwamishinan ayyuka na jihar Kano, Mu'azu Magaji ya gasgata rahoton da Dan Bello ya fitar cewa Murtala Garo ya saci kudin jama'a
  • Dan Bello ya yi ikirarin cewa tsohon kwamishinan kananan hukumomi lokacin Ganduje ya saci N10bn ya sayi kadara a birnin Makkah
  • Mu'azu Magaji ya ce ko a lokacin da ya ke kwamishina sai da ya kori kamfanin Murtala Garo, lamarin da ya jawo rigimarsa da matar Ganduje

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Kano - Mu'azu Magaji, tsohon kwamishinan ayyukan na Kano a lokacin gwamnatin tsohon gwamna Abdullahhi Umar Ganduje ya magantu kan bidiyon Dan Bello.

A cikin wani bidiyo da Dan Bello (wanda asalin sunansa Bello Habib Galadanchi) ya fitar, ya zargi tsohon kwamishinan Kano, Murtala Sule Garo da satar kudin gwamnati.

Kara karanta wannan

Zanga zanga: Tsohon gwamnan Kano ya gano bakin zaren, ya aika saƙo ga Tinubu

Kwamishinan Ganduje ya yi magana kan badakalar Murtala Garo a bidiyon Dan Bello
Bidiyon Dan Bello: Kwamishinan Ganduje ya gaskata badakalar Murtala Garo: Hoto: Murtala Sule Garo, Mu'azu Magaji
Asali: Facebook

Dan Bello ya zargi Murtala da rashawa

A cikin bidiyon wanda Dan Bello ya wallafa a shafinsa na X, ya yi ikirarin cewa Murtala Sule Garo ya saci akalla Naira biliyan 10 a lokacin da yake kwamishinan kananan hukumomi.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Bello ya yi ikirarin cewa Murtala Garo ya rika karbar Naira miliyan 5 daga kowace karamar hukumar Kano a duk wata da sunan za a biya kudin dizal na ruwan da ake tacewa a jihar.

Sai dai Dan Bello ya ce babu dizal din da ake saya domin Murtala Garo na amfani da kamfanoninsa biyu, MJ da AU a matsayin wadanda ke sayarwa gwamnati man.

Bello ya ce MJ da AU na turawa wasu 'yan canji a kasuwar Wapa kudin domin mayarwa zuwa Riyal, inda ake turawa kamfanin 'Next Vision' da ke birnin Makkah.

Kara karanta wannan

N57bn: Gwamnati ta sake lafta wasu zarge zarge kan shugaban APC, Abdullahi Ganduje

A cewar dan jaridar, kamfanin N.V ya sayawa Murtala Garo wani bangare na wani babban otel a kusa da dakin Ka'abah, bayan da tsohon kwamishinan ya tura akalla Naira biliyan 10.

Kwamishinan Ganduje ya gaskata Dan Bello

Bayan fitar wannan bidiyo na Dan Bello, 'yan soshiyal midiya sun cika da mamakin irin badakalar da tsohon kwamishinan Kano ya tafka, inda wasu ke ganin karya ce kawai.

Sai dai tsohon kwamishinan ayyuka na jihar, Mu'azu Magaji, ya gaskata rahoton Dan Bello, inda ya ce badakalar ce ta hada shi fada da uwar gidan Ganduje.

A wata wallafa da ya yi a shafinsa na Facebook, tsohon kwamishinan ayyukan ya ce:

"Kai jama’a, shin da sauran imani kuwa? Koda yake daga na gaba ake gane zurfin ruwa.
"Mu je zuwa! Mun yi ta babatu kan wannan dan halin a gwamnatin mu amma aka mai damu mahaukata. Asali ma saida aka ga bayanmu kan ba a son jin gaskiya. To an zo wurin!"

Kara karanta wannan

Zanga zanga: Matashi a Kano ya yi barazanar kashe kakakin rundunar 'yan sanda

Wani Sulaiman Musa Tofa ya tambayi Mu'azu: "Jagora na ga kaima ka rike kwammishinan ayyuka a baya," sai jagoran na 'Win Win' ya ba shi amsa da:

"Ai ko ni shaida ne don sai da na kori wannan kamfanin a ma'aikatar ayyuka kan badakalar dizal, wannan dama wasu dalilan sune farkon rigimar mu da Gwaggo."

Kalli bidiyon Dan Bello a nan kasa:

'Dan El-Rufai ya ba Dan Bello shawara

A wani labarin, mun ruwaito cewa daya daga cikin 'ya'yan tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru El-Rufai ya nemi Dan Bello (Bello Galadanchi) da ya yi hattara da 'yan siyasa.

Bashir El-Rufai ya ce ya kamata Dan Bello ya rika bi a hankali a bidiyoyin fallasa 'yan siyasa da yake yi, la'akari da cewa shi kansa yana cikin masu son tsohon dan jaridar.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.