An Barke da Murna da Fitaccen Dan Kasuwa a Arewa Ya Rage Farashin Siminti

An Barke da Murna da Fitaccen Dan Kasuwa a Arewa Ya Rage Farashin Siminti

  • Wani mai amfani da kafar sadarwa ta X ya wallafa cewa kamfanin siminti na Dahiru Mangal ya fara siyar da siminti a farashi mai sauki
  • Matashin mai suna Maleek Anas ya wallafa a shafin X cewa ya sayi buhunan siminti guda biyu kan kudi N6,000
  • Wasu mutane da dama sun fara bincikar wurin da za su samu damar siyan simintin yayin da ake fama da tsadar rayuwa

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Kogi - Fitaccen dan kasuwa a Najeriya, Dahiru Mangal ya fara siyar da siminti a kamfaninsa da ke jihar Kogi.

Kamfanin mai suna Mangal Cement Company mallakar attajiri dan jihar Katsina an kashe masa kudi kimanin $1.5bn.

Kara karanta wannan

Tsadar rayuwa: Jigon PDP ya fadi yadda Tinubu zai magance matsalolin Najeriya

Mutane sun barke da murna bayan rage farashin siminti
Wani matashi ya wallafa yadda ya sayi siminti a kamfanin Dahiru Mangal kan N6,000 kacal. Hoto: Nurphoto.
Asali: Getty Images

Matashi ya fadi yadda ya sayi siminti

Wani mai amfani da kafar sadarwa ta X, Maleek Anas ya wallafa wasu buhunan siminti guda biyu da ya siya a farahin mai rahuwa.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Anas ya wallafa buhunan guda biyu inda ya ce ya sayi kowane kan N6,000 kacal a kamfanin.

"Farashin simintin Mangal N6,000 kacal ake siyarwa."

- Maleek Anas

Siminti: Mutane da dama sun yi martani

@Melebroz 1:

"Wannan mataki ne mai kyau, sai dai ina tunanin kamfanin Mangal ba zai iya samar da siminti buhuna 200 ba a rana."

@YDutsun44451:

Muna godiya Mangal da ka kawo gasa a kasuwancin siminti, ya kamata ka rage farashin saboda ka kara samun kwastomomi."

@de_profde_chef:

Shin za a iya ragewa zuwa N4,000 kacal? sannan ya yanayin karfin simintin yake."

@Abbadanejo:

"Ina son siyan buhu 50, shin akwai wanda zai taimakamin da haka?"

Kara karanta wannan

Doguwa v Jibrin: 'Dan majalisar APC ya karyata zargin kashe rayuka a Kano domin cin zabe

Kamfanoni sun ki rage farashin siminti

A wani labarin, Kwamitin da ke bincike kan farashin siminti ya bayyana halin da ake ciki kan zama da majalisar wakilai za ta yi da kamfanonin siminti.

A ranar Litinin 20 ga watan Mayun 2024 Majalisar ta gayyaci manyan kamfanonin domin su gurfana a gabanta kan shawo tsadar siminti a Najeriya.

Shugaban kwamitin binciken farashin siminti da majalisar ta kafa, Jonathan Gaza Gefwi ya ce suna fakewa da umurnin kotu wurin kin amsa gayyatarsu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.