Kudin da Kowane Gwamna Ya Tashi da Su da Tinubu Ya Raba Naira Biliyan 430 a Jihohi 34

Kudin da Kowane Gwamna Ya Tashi da Su da Tinubu Ya Raba Naira Biliyan 430 a Jihohi 34

  • Gwamnatin tarayya ta bayyana cewa ta rabawa jihohi wasu makudan kudi a karkashin tsarin NG-Cares
  • Gwamnonin Zamfara, Nasarawa, Filato da Gombe su na cikin wadanda suka samu kudi masu yawan gaske
  • Ministan kasafin kudi ya fadawa duniya kason da aka aika, Anambra da Kaduna ne kadai ba samu kudin nan ba

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

M. Malumfashi ya shafe shekaru ya na kawo labaran Hausa musamman na siyasa, addini, tarihi, wasanni da al’ada

Abuja – Gwamnatin tarayya ta fitar da sama da N438bn, ta maidawa jihohi a karkashin wani tsarin farfado da tattalin arziki.

Jami’in yada labarai da hulda da jama’a na ofishin NG-Cares, Suleiman Odapu, ya tabbatar da haka a wani jawabi da ya fitar kwanaki.

Tinubu da Gwamnoni
Gwamnatin tarayya ta rabawa Gwamnonin jihohi kudin NG-Cares Hoto: @OfficialABAT
Asali: Twitter

Za a samu wannan bayani a adireshin NG-Cares na yanar gizo wanda daga cikin shi ne Legit ta hada rahoton abin da aka ba jihohi.

Kara karanta wannan

Ana tsaka da bankadar Dan Bello, Tinubu ya dakatar da aikin hanyar Kano zuwa Maiduguri

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Zamfara ta fi kowa sa'ar kudin NG-Cares

Jihar Zamfara kamar yadda gwamna Dauda Lawal Dare ya sanar, ta fi kowa samun kaso mai tsoka daga wannan kudi, ta karbi N49bn.

Nasarawa da Filato duk daga Arewa maso tsakiya ne su ka zo na biyu da na uku. The Guardian ta tabbatar da wannan labari a rahotonta.

Jihohin da suka rasa kason NG-Cares

Jihohin Anambra da Kaduna ne kadai ba su samu komai daga kason ba domin ba su iya gabatar da wani sakamako da ake bukata ba.

Channels ta rahoto wasu gwamnoni sun karyata lamarin, su ka ce gwamnatin tarayya ba ta aiko masu da sisin kobo ba zuwa yanzu.

Kamar yadda Ministan kasafin kudi ya sanar a jaridar Daily Trust, ga abin da aka ba jihohi:

NG-Cares: Nawa aka rabawa jihohi?

1. Delta

Kara karanta wannan

NNPC ke yiwa tattalin arziki zagon kasa? Kyari ya wanke kamfanin Najeriya

N13,268,320,155.81

2. Abia

N12,175,577,893.70

3. Bayelsa

N10,830,587,695.70

4. Yobe

N10,172,244,387.67

5. Kwara

N9,915,101,215.91

6. Osun

N9,562,512,549.27

7. Bauchi

N7,304,665,994.92

8. Kogi

N6,903,713,160.77

9. FCT

N6,773,326,717.84

10. Ebonyi

N6,255,864,530.97

11. Enugu

N6,191,959,222.93

12. Kano

N6,154,448,839.35

13. Oyo

N5,966,675,258.19

14. Borno

N5,898,270,783.50

15. Jigawa

N5,770,132,061.00

16. Lagos

N5,569,060,730.14

17. Taraba

N5,508,762,972.80

18. Ekiti

N5,507,202,258.33

19. Edo

N5,122,103,650.09

20. Benue

N4,908,421,973.10

21. Akwa Ibom

N2,430,830,532.46

22. Ogun

2,125,069,028.52

23. Zamfara

N49,182,347,834.58

24. Nasarawa

N27,204,679,444.17

25. Plateau

N26,312,588,262.79

26. Gombe

N25,305,166,261.04

27. Kebbi

N21,589,480,398.09

28. Rivers

N19,517,766,804.45

29. Niger

N17,769,395,563.89

30. Bauchi

N17,535,952,985.60

31. Katsina

N15,455,420,486.35

32. Imo

N15,408,252,449.34

33. Sokoto

N14,177,508,862.60

34. Cross River

N20,670,241,709.19

35. Ondo

N13,925,262,355.18

Tarihin kirkiro jihohi a Najeriya

An samu rahoton yadda Janar Yakubu Gowon ya fara kirkiro jihohi a tarihi shekarar 1967 domin karya C. Odumegwu Ojukwu.

Kafin Ibrahim Babangida wanda aka fi sani da IBB ya bar mulki ya amince da karin jihohi sama da 10 a shekarar 1987 da 1991.

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng