Shugaba Tinubu Ya Ba Jami'an Tsaro Umarni Yayin da Ake Ci Gaba da Zanga Zanga

Shugaba Tinubu Ya Ba Jami'an Tsaro Umarni Yayin da Ake Ci Gaba da Zanga Zanga

  • Bola Ahmed Tinubu ya buƙaci kamfanonin da ke aikin haƙar ma'adanai su ba da fifiko wajen kula da lafiyar ƴan Najeriya
  • Shugaban ƙasa Tinubu ya kuma umarci jami'an tsaro da su ƙara ƙaimi wajen kawo ƙarshen masu haƙar ma'adanai ba bisa ƙa'ida ba
  • Tinubu ya bayyana cewa kawo ƙarshen masu haƙar ma'adanan ba bisa ƙa'ida ba zai taimakawa tattalin arziƙin ƙasar nan

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

FCT, Abuja - Shugaban ƙasa Bola Tinubu ya umurci jami’an tsaro da su ƙara ƙaimi wajen murƙushe masu haƙar ma’adinai ba bisa ƙa’ida ba a faɗin ƙasar nan.

Shugaba Tinubu ya ce akwai masu haƙar ma'adanai ba bisa ƙa'ida ba a faɗin ƙasar nan waɗanda tilas ne jami’an tsaro su ga bayansu.

Kara karanta wannan

Ba a mugun sarki: Al Mustapha ya bayyana hakikanin makiyan Shugaba Tinubu

Shugaba Tinubu ya umarci a kawo karshen hakar ma'adanai ba bisa ka'ida ba
Shugaba Tinubu ya umarci jami'an tsaro su kawo karshen hakar ma'adanai ba bisa ka'ida ba Hoto: @OfficialABAT
Asali: Twitter

Bola Tinubu ya ba da umarni

Shugaba Tinubu ya kuma ce gwamnatinsa za ta tabbatar da cewa kamfanonin da ke haƙo ma'adanai sun ba da fifiko wajen kula da lafiyar ƴan Najeriya.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da hadiminsa, Dada Olusegun ya sanya a shafinsa na X.

Shugaban ƙasan ya bayyana hakan ne lokacin da yayin da yake sauraron wata lacca da ɗaliban kwalejin tsaro ta ƙasa (NDC) suka gabatar ranar Alhamis a birnin tarayya Abuja. 

"Muna da masu haƙar ma'adanai ba bisa ƙa'ida ba a ƙasar nan. Dole ne mu kawo ƙarshensu. Ku jami'an tsaro kun fi fahimtar muhimmancin hakan fiye da fararen hula."
"Muna tsammanin cewa ta hanyar ƙoƙarinku, za mu samu isassun albarkatun ƙasa da muke buƙata domin tabbatar da cewa mun samu tattalin arziƙi wanda zai zauna da ƙafafunsa."

Kara karanta wannan

Ana cikin zanga zanga, Tinubu ya aika sako mai ratsa zuciya ga 'yan Najeriya

- Bola Tinubu

Shugaba Tinubu ya kuma ba ƴan tawagar tabbacin cewa gwamnatinsa za ta kammala aikin hedkwatar NDC da ke birnin tarayya Abuja.

Karanta wasu labaran kan Tinubu

An bayyana maƙiyan shugaba Tinubu

A wani labarin kuma, kun ji cewa Manjo Hamza Al-Mustapha mai ritaya ya bayyana haƙiƙanin maƙiyan shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu.

Dogarin na Sani Abacha ya bayyana cewa hadiman Tinubu su ne haƙiƙanin maƙiyansa saboda yadda suka bari aka gudanar da zanga-zanga a ƙasar nan.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng