"Mun Tsaurara Matakan Tsaro,” Gwamnatin Kano ta Sassauta Dokar Hana Fita

"Mun Tsaurara Matakan Tsaro,” Gwamnatin Kano ta Sassauta Dokar Hana Fita

  • Gwamnatin Kano ta sassauta dokar hana fita ta awa 24 da ta sanya, inda a yanzu aka mayar da dokar daga karfe 6 na safe zuwa 6 na yamma
  • Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Salman Dogo ne ya sanar da hakan a ranar Talata bayan kammala taron majalisar tsaron jihar
  • Kwamishinan 'yan sandan ya bukaci mazauna jihar da su ba jami'an tsaron da aka girke a ciki da wajen birnin Kano goyon baya da hadin kai

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Kano - Gwamnatin jihar Kano ta sake waiwayar dokar hana fita ta awa 24 da ta sanya a fadin jihar biyo bayan zanga-zangar yunwa da ta rikide zuwa tashin hankali.

Kara karanta wannan

Kano: An kama hatsabibin 'barawon' da ya fitini mutane da fashi zai tsere bayan sace N15m

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Salman Dogo ne ya sanar da hakan a ranar Talata bayan kammala taron majalisar tsaron jihar da Gwamna Abba Yusuf ya jagoranta.

Gwamnatin Kano ta yi magana kan dokar hana fita da ta sanya
Gwamnatin Kano ta sassauta dokar zaman gida da ta sanya a fadin jihar. Hoto: @Noble_Hassan
Asali: Twitter

Gwamnatin jihar Kano ta ce dokar hana fita a jihar yanzu ta fara daga karfe 6 na safe zuwa 6 na yamma, kamar yadda sanarwar mai tallafawa gwamnan, Hassan Sani Tukur ya wallafa a shafinsa na X.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Kano: An sassauta dokar hana fita

Mai sharhi kan lamuran tsaro, Zagazola Makama ya wallafa cikakkiyar sanarwar kwamishinan 'yan sanda a shafinsa na X, inda ya ruwaito Salman Dogo yana cewa:

"Gwamna Abba Yusuf, bayan tattaunawa mai zurfi da ‘yan majalisar tsaron jihar ya yanke shawarar sake sassauta dokar hana fita daga karfe 6 na safe zuwa 6 na yamma.
"An dai sassauta dokar hana fitar ne domin dawo da zaman lafiya a jihar, kuma jami’an tsaro za su kasance a dukkan sassan jihar domin tabbatar da doka da oda."

Kara karanta wannan

Wani gwamnan Arewa ya rage awannin hana fita, an gurfanar da masu zanga zanga a kotu

An tsaurara matakan tsaro a Kano

Kwamishinan 'yan sandan ya bukaci mazauna jihar da su ba jami'an tsaron da aka girke a ciki da wajen birnin Kano hadin kai domin dawo da zaman lafiya.

Ya kuma bukaci mazauna jihar da su rika komawa gidajensu a kan lokaci, inda ya ba su tabbacin cewa za a kara sassauta dokar gwargwadon tsaron da aka samu.

"Jami’an tsaro za su kasance a dukkan sassan jihar domin tabbatar da doka da oda, ana neman jama'a su ba jami'an hadin kai yayin gudanar da ayyukansu."

- A cewar kwamishinan.

Gwamnan Kano ya dauki matakai kan zanga-zanga

A wani labarin, mun ruwaito cewa gwamnatin Kano ta nuna takaicinta kan yadda wasu yan daba suka kwace zanga-zangar lumana suka mayar da ita ta ta'addanci a fadin jihar.

Domin magance matsalar zanga-zangar, Gwamna Abba Yusuf ya dauki matakai shida ciki har da bude cibiyoyin horar da matasa sana'o'in dogaro da kansu da kula da masu shaye-shaye.

Kara karanta wannan

Zanga zanga: Gwamnatin Kano ta ɗauki matakai 6, ta yi magana kan ɗaga tutar Rasha

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.