Cigaba 6 da Aka Samu da ba a Maganarsu Bayan Tinubu Ya Karbi Mulki a Hannun Buhari

Cigaba 6 da Aka Samu da ba a Maganarsu Bayan Tinubu Ya Karbi Mulki a Hannun Buhari

Abuja - Daga lokacin da aka ce Bola Ahmed Tinubu ya karbi mulki, an yi ta kokarin kawo sauyi a bangaren tattalin arziki a kasar nan.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

M. Malumfashi ya shafe shekaru ya na kawo labaran Hausa musamman na siyasa, addini, tarihi, wasanni da al’ada

Duk da mafi yawan jama’a su na kuka da tsadar rayuwa, hauhawar farashi da tashin kudin fetur, akwai wasu nasarorin da aka samu.

Bola Tinubu
Shugaba Bola Tinubu yana kokarin gyara tattalin arzikin Najeriya Hoto: Abdulaziz Abdulaziz
Asali: Facebook

Kwanakin baya Olusegun Dada, ya jero wasu cigaba a X da aka samu a tattalin arziki cikin shekara guda da shugaban kasar ya yi a ofis.

Mista Olusegun Dada yana cikin masu taimakawa Bola Tinubu a kafofin sada zumunta. Hadimin shugaban Najeriyan ya jero abubuwa 6:

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Kara karanta wannan

Zanga zanga ta koma fitina: An kashe mutum 1 yayin da aka babbake gidan mai a Kano

Nasarorin Bola Tinubu a fannin tattalin arziki

1. Asusun kudin kasar waje

Daga $33.09bn a karshen shekarar 2023, alkaluman babban bankin CBN sun nuna asusun kudin kasar wajen Najeriya ya karu a yanzu.

A cewar Dada, kudin kasar wajen ya kai $35.05bn a watan Yulin nan. The Nation ta ce zuwa yanzu kudin cikin asusun ya zarce $35.77bn.

2. Karin albashi

A yayin da Bola Tinubu ya hau karagar mulki, N30, 000 ne mafi karancin albashin talaka, amma yanzu gwamnati ta maida shi N70, 000.

Wannan kari na sama da 100% bai fara aiki ba tukuna, amma tuni aka sa hannu.

3. Bashin Najeriya

Idan aka kamanta kason bashin da ake bin Najeriya da kudin shiga kafin Yunin 2023, an matukar cigaba a karkashin mulkin Bola Tinubu.

A 2023, kason kudin shiga da bashin da ke wuyan kasar ya kai 97%, yanzu alkaluma sun ce bashi bai wuce 67% na kudin da aka aro ba.

Kara karanta wannan

Litar fetur ta koma N1,300 a wajen ƴan bumburutu, NNPCL ya aika sako ga ƴan Najeriya

4. Hako danyen mai

Hukumar NUPRC ta ce a yanzu Najeriya tana hako ganguna miliyan 1.61 na danyen mai a kowace rana, kuma za a iya zarce hakan.

Punch ta ce bayanin Injiniya Gbenga Komolafe sun nuna an samu cigaba daga ganguna 900, 000 da ake iya hakowa a watan Mayun 2023.

5. Bashin kudin kasar waje

A watan Mayun 2024, an rahoto Yemi Cardoso ya na cewa bankin CBN ya biya bashin kudin kasar waje da kamfanoni suke bin kasar.

Olayemi Cardoso ya ce biyan wadannan kudi $7.5bn da aka gada zai taimakawa tattali.

6. Bashin cikin gida

Ministan tattalin arziki, Wale Edun ya yi alkawari za a gujewa karbar bashi a hannun CBN kamar yadda Muhammadu Buhari ya rika yi.

A lokacin da aka canza mulki a bara, CBN ta na bin gwamnatin tarayya bashin N26tr da aka buga mata, yanzu bashin kudin ya koma N16tr.

Kira ga Tinubu da gwamnoni a jihohi

Kara karanta wannan

Sheikh Abdulaziz Dutsen Tanshi ya fadawa Tinubu mataki 1 da zai cire talaka daga wahala

A baya an kawo rahoto cewa Farfesa Ahmad Bello Dogarawa ya yi kira ga duka shugabannin da ke mulki a hudubar ranar Juma’ar nan a Zariya.

Babban malamin musuluncin ya yi kira ga masu mulki da shugabannin hukumomi da kuma talakawa su ji tsoron Allah a duka al'amuransu.

A hudubar da ya gabatar, limamin ya ce duk shugaban da bai yi adalci ba, ba zai ji kanshin aljannah ba idan an tafi filin kiyama a gobe lahira.

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng