Zanga Zanga: An Kashe Mutane 14, An Kama 'Yan Shi'a Cikin Wadanda Ake Zargi da Laifi

Zanga Zanga: An Kashe Mutane 14, An Kama 'Yan Shi'a Cikin Wadanda Ake Zargi da Laifi

  • Zanga zangar da matasa suka fara gudanarwa a Najeriya kan tsadar rayuwa ta jawo asarar rayuka da dukiya mai dimbin yawa
  • An ruwaito cewa an kashe mutane da dama a jihohin Kaduna, Borno, Neja da sauransu ciki har da jami'an tsaro yayin zanga zangar
  • Rundunar yan sanda ta kama mutane da dama da ake zargi da aikata laifuffuka da dama a sassan Najeriya yayin zanga zangar

Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.

Nigeria - Zanga zangar adawa da tsadar rayuwa a Najeriya ta jawo asarar rayuka da dukiya mai yawa a ranar farko.

Rahotanni sun nuna cewa zanga zangar ta rikide ta koma tarzoma a jihohi da dama musamman a Arewacin Najeriya.

Kara karanta wannan

Zanga zanga: Matasa sun cinnawa sakatariya wuta, 'yan sanda sun dauki mataki

Zanga zanga
An kashe mutane 14 yayin zanga zanga. Hoto: NurPhoto
Asali: Getty Images

Jaridar Vanguard ta ruwaito cewa rundunar yan sanda ta yi nasarar cafke da dama daga cikin wadanda suka fara sace sace a lokacin zanga zangar.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

An kashe mutane 14 a zanga zanga

A ranar farko ta zanga zangar adawa da tsadar rayuwa a Najeriya an kashe mutane akalla 14 a sassan Najeriya, musamman a Arewa.

A jihar Neja, an kashe mutane shida a yankin Suleja yayin da aka kashe mutane hudu a gidan mai a Maiduguri, babban birnin jihar Borno.

Haka zalika an kashe mutane uku a jihar Kaduna, sannan aka kashe wani dan kasuwa a shagonsa a Yauri da ke jihar Kebbi.

Zanga zanga: An zargi yan Shi'a da tarzoma

Kakakin rundunar yan sanda a jihar Kaduna, ASP Mansir Hassan ya zargi yan Shi'a da mayar da zanga zangar lumana tarzoma a Kaduna.

Kara karanta wannan

Jihohin Arewa da aka sanya dokar hana fita ta awa 24 sun kai 4, an samu cikakken bayani

ASP Mansir Hassan ya ce an fara zanga zangar lami lafiya kafin su shigo su fara tayar da hankali daga nan kuma lamari ya rikice a jihar.

Rahoton Channels Television ya nuna cewa rundunar yan sanda a jihar Kaduna ta yi nasarar cafke mutane 25 da ake zargi da yin sace sace a lokacin zanga zangar.

Matasa sun yi rikici da yan sanda

A wani rahoton, kun ji cewa matasan Najeriya suka cika titunan domin yin zanga zangar adawa da tsadar rayuwa a kusan dukkan jihohin kasar.

A jihar Kaduna an samu rashin jituwa tsakanin jami'an tsaro da masu zanga zanga inda har lamarin ya kai ga yin harbi sama.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ibrahim Yusuf avatar

Ibrahim Yusuf (Hausa Editor) Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum. ibrahim.yusuf@corp.legit.ng