Kwanaki 10: Lauya ya Nemi Alfarma, Ya Roki Masu Zanga Zanga su Rage Tsawon Lokaci

Kwanaki 10: Lauya ya Nemi Alfarma, Ya Roki Masu Zanga Zanga su Rage Tsawon Lokaci

  • Daga yau, 1 Agusta 2024 ne masu zanga-zanga a Najeriya za su fara fita tituna domin nuna fushinsu a kan kamun ludayin gwamnati
  • Masu zanga-zangar sun bayyana aniyar cewa za su gudanar da ita har tsawon kwanaki 10 domin tabbatar da cewa gwamnati ta saurare su
  • Amma wani lauya a kasar nan, Ebun Olu Adegboruwa ya roki matasan Najeriya su rage kwanakin da za su gudanar da zanga-zanga

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

Jihar Legas - Yayin da ake sa ran fara zanga-zangar gama gari a fadin Najeriya daga yau Alhamis 1-10 Agusta, 2024, an roki matasan kasar nan.

Kara karanta wannan

Abin da gwammoni 6 suka faɗa game da zanga zangar da aka fara yau a Najeriya

Wani lauya, Ebun Olu Adegboruwa ya ce matasan su yi hakuri, su kuma rage kwanakin zanga-zanga daga kwanaki 10 zuwa kwana ɗaya tal.

Anadolu Agency
Lauya ya nemi a rage kwanakin zanga-zanga Hoto: Anadolu Agency
Asali: Getty Images

Za a rage kwanakin zanga-zanga?

Channels Television ta tattaro cewa lauyan mai matsayin SAN ya yaba da jajircewar matasan Najeriya wajen tabbatar da cewa gwamnati ta ji kukansu.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Amma ya yi rokon a rage kwanakin daga 10 zuwa daya ko kwanaki uku zai taimaka sosai wajen ba wa gwamnati damar duba matsalolin da aka zayyana.

"A yi zanga-zanga cikin lumana," Lauya

Babban lauyan a kasar nan, Ebun Olu Adegboruwa ya nemi matasan Najeriya da za su fara zanga-zanga a yau Alhamis da su gudanar da ita cikin lumana.

The Cable ta wallafa cewa dagiyar da rundunar 'yan sanda ta yi na cewa akwai bata-gari da ke son shiga rigar zanga-zanga ya nuna cewa gwamnati na son hana fita.

Kara karanta wannan

"Muna can muna cin abinci," Shugaban Majalisa ya ta da ƙura kan zanga zanga da ake shirin yi

Ya zargi gwamnati da kokarin dauko 'yan saba da kanta wajen hautsina zanga-zangar, saboda haka ya bukaci matasan su fito cikin lumana da tsari.

Gwamnati ta fadi matsalar zanga-zanga

A baya kun ji cewa gwamnatin Bola Ahmed Tinubu ta fadi dalilin da ya sa ta nemi matasan kasar nan su hau teburin tattaunawa a maimakon zanga-zanga.

Sakataren gwamnati, George Akume ya bayyana cewa sun hango yiwuwar 'yan Boko Haram da sauran 'yan binga za su shiga cikin masu zanga-zanga domin aika-aika.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano.