Ana Shirin Fita Zanga Zanga, Matasa Sun Farmaki Mota Makare da Kayan Abinci

Ana Shirin Fita Zanga Zanga, Matasa Sun Farmaki Mota Makare da Kayan Abinci

  • An yi babban asara bayan wasu miyagu sun farmaki babbar motar bas makare da kayan abinci a jihar Cross River
  • Miyagun sun fakaici motar da ke kan hanyarta ta zuwa sakatariyar ƴan jaridu a jihar inda suka tafka musu barna
  • Hakan na zuwa ne yayin da ake cikin wani irin hali na tsadar rayuwa da kuma shirin fita zanga-zanga a fadin kasar

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Cross River - Miyagu akalla 100 ne suka farmaki motar bas dauke da kayan tallafi a jihar Cross River.

Bas din makare take da kayan abinci na kungiyar ƴan jaridu a jihar da ta nufi sakatariyar kungiyar.

Kara karanta wannan

Adawa da gwamnatin Tinubu: Akpabio ya fallasa wadanda suka dauki nauyin zanga zanga

Miyagu sun tafka barna bayan hari kan motar abinci
Wasu matasa sun farmaki motar bas cike da kayan abinci a jihar Cross River. Hoto: Legit.
Asali: Original

Matasa sun kai hari kan motar abinci

Vanguard ta tattaro cewa matasan sun yi nasarar kwashe wasu daga cikin kayayyakin abinci bayan fasa tagogin motar a jihar.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Daraktan yada labarai na hukumar agajin gaggawa ta NEMA a jihar, James Anam shi ya tabbatar da haka ga manema labarai.

Direban motar mai suna Joseph Akpaenin da kyar ya sha da rayuwarsa inda ya ce an dauke masa wayar salula yayin farmakin, Daily Post ta tattaro.

Barnar da aka tafka yayin farmakin

Akpaenin ya ce miyagun sun cigaba da kwashe kayan abincin da ke zuba daga motar inda a lokacin ne ya samu ya tsira da rayuwarsa.

Da yawa daga cikin wadanda suke tawagar sun samu raunuka cikin har da dan jarida daga Tribune inda suke kwance a gadon asibiti.

Hakan bai rasa nasaba da halin kunci da ake ciki na tsadar rayuwa da matsanancin talauci.

Kara karanta wannan

'Yan siyasa da kungiyoyi da ke goyon bayan zanga zanga da wadanda suka kushe tsarin

"Na biya bukatun masu zanga-zanga" - Tinubu

Kun ji cewa Shugaban ƙasa, Bola Tinubu ya tabbatar da cewa ya biya mafi yawan bukatun matasa masu shirin zanga-zanga.

Tinubu ya ce ya dauki wasu matakai masu muhimmanci wadanda za su kawo dauki ga al'umma baki daya duba da halin da ake ciki.

Wannan na zuwa ne yayin da matasa ke shirin fita zanga-zanga a kasar musamman saboda halin kunci da kuma tsadar rayuwa.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.