Bola Tinubu Ya Gano Masu Ɗaukar Nauyin Zanga Zanga, Ya Faɗawa Matasa Gaskiya

Bola Tinubu Ya Gano Masu Ɗaukar Nauyin Zanga Zanga, Ya Faɗawa Matasa Gaskiya

  • Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ya ƙara yin tsokaci kan masu ɗaukar nauyin zanga-zanga da ake shirin yi a watan da ke tafe
  • Bola Tinubu ya bayyana cewa masu ɗaukar nauyin ba mazauna ba ne kuma suna shirya komai tare da tunzura mutane daga ƙasashen ketare
  • Shugaba Tinubu ya faɗi haka ne yayin da ya karɓi bakuncin Malaman Addinin Musulunci a Aso Villa ranar Alhamis

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja - Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ya yi iƙirarin cewa masu ɗaukar nauyin zanga-zangar da ake shirin yi ba su ƙishin Najeriya.

Tinubu ya bayyana haka ne ranar Alhamis a fadar shugaban ƙasa yayin da ya karɓi bakuncin Malaman Addinin Musulunci ƙarƙashin jagorancin Sheikh Abdullahi Bala Lau.

Kara karanta wannan

Zanga zanga: Jigon APC ya fadi abin da 'yan Najeriya ya kamata su yi wa Tinubu

Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu.
Bola Tinubu ya ce masu ɗaukar nauyin zanga zangar da ake shirin ba su kaunar Najeriya Hoto: Ajuri Ngelale
Asali: Facebook

Sai dai shugaban ƙasar bai bayyana sunaye da bayanan masu ɗaukar nauyin zanga-zangar ba, kamar yadda Channels tv ta ruwaito.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Tinubu ya faɗi masu ɗaukar nauyin zanga-zanga

Shugaba Tinubu ya ce masu zugawa da matsa lamba dole sai an yi wannan zanga-zangar suna da fasfon wasu ƙasashen kuma ta intanet suke yin tarukansu.

"Masu ɗaukar nauyin zanga-zangar nan ba su kaunar Najeriya, babu sauran ɓurɓushin kishin ƙasa a zuƙatansu, ba su san komai ba game da zama ɗan ƙasa.
"Su na da katin zama a wasu kasashen ƙetare, daga can suke kitsa komai ta intanet. Ba mu son abin da ya faru a Sudan ya faru a Najeriya.
"Batu ne na yunwa ba jana'iza ba, dole mu yi taka tsan-tsan, mu san wasan da muke takawa a siyasa, mu kauce wa siyasa ƙiyayya da gaba. Ta intanet suke yin taruka suna ƙara tunzura mutane."

Kara karanta wannan

Zanga zangar adawa da Tinubu: Jam'iyyar APC ta dauki muhimmin mataki

- Bola Tinubu.

Shugaba Tinubu ya ƙara da cewa duk zanga-zangar da nufin nuna fushi da ƙiyayya, tana iya riƙeɗewa zuwa tashin-tashina kuma ta jawo koma baya a kasa, Daily Trust ta rahoto.

Malamai sun roƙi matasa su janye zanga-zanga

A wani rahoton kun ji cewa Malaman addinin Musulunci a Najeriya sun isar da koken talakawa ga shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu a fadar Aso Villa ranar Alhamis

Bayan ganawa da Tinubu, malaman sun roƙi ƴan Najeriya musamman matasa su haƙura sun janye zanga-zangar da suke shirin yi a watan Agusta

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262