Wahalar Fetur Za Ta Tsananta, Dillallan Mai Sun Shiga Yajin Aiki a Wasu Jihohin Najeriya

Wahalar Fetur Za Ta Tsananta, Dillallan Mai Sun Shiga Yajin Aiki a Wasu Jihohin Najeriya

  • Wani abu mai kama da yajin aiki ya faru a Oyo da Osun inda dillalan man fetur suka rufe gidajen mai a fadin jihohin biyu
  • Kungiyoyin 'yan kasuwar man na IPMAN da NUPENG sun ce 'yan sanda sun matsawa mambobinsu da karbar kudi da cin zarafi
  • A cewar 'yan kasuwan, ba za su bude gidajen main ba har sai an dakatar da 'yan sanda daga hantarar mambobinsu a manyan hanyoyi

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Mambobin kungiyoyin dillalan man fetur na IPMAN da NUPENG a jihohin Oyo da Osun sun dakatar da aiki tare da rufe gidajen mansu.

Dillalan man, a wani taron gaggawa da suka gudanar a Ibadan ranar Asabar, sun ce sun yanke shawarar ne saboda “Karbar kudi da hantarar da ‘yan sanda ke yiwa mambobinsu."

Kara karanta wannan

Harka ta lalace: Mai aukuwa ta auku, an ba 'yan kasar waje wa'adin barin Sudan cikin gaggawa

IPMAN da NUPENG sun yi magana kan rufe gidajen mai a Oyo da Osun
Dillalan man fetur sun rufe gidajen mai kan cin zarafin 'yan sanda. Hoto: Benson Ibeabuchi
Asali: Getty Images

IPMAN. NUPENG sun shiga yajin aiki

Taron ya samu halartar shugaban defo na Ibadan, Mutiu Bukola da Hammed Hamzat shugaban direbobin tankar man fetur (PTD) reshen kungiyar NUPENG, inji rahoton The Cable.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sauran wadanda suka halarci taron sun hada da Surajudeen Adegoke, shugaban kungiyar ‘yan kasuwar mai ta NUPENG, da Olalekan Lawal, mataimakin shugaban kungiyar IPMAN.

A cewar jaridar The Punch, sun yi Allah wadai da cin kashin da ‘yan tawagar sa ido na sufetan ‘yan sanda (IGP) suke yiwa mambobinsu a kan manyan hanyoyi.

Yaushe za a sake bude gidajen man?

Sun ce tsangamar da jami'an tsaron ke nunawa mambobinsu ne ya jawo babban gibi wajen dakon man fetur daga defo zuwa gidajen mai na fadin jihohin biyu.

Mista Bukola wanda ya yi magana a madadin kungiyoyin ya yi kira da a gaggauta kawo karshen cin zarafi da karbar kudaden da ake yi wa mambobin kungiyoyinsu.

Kara karanta wannan

Kawo karshen tsadar mai: Dillalan man fetur sun ba da shawarar yadda man fetur zai koma N620

Ya ce ba za su bude gidajen man ba ba har sai an magance matsalolin.

NNPC zai nemo sabon bashin $2bn

A wani labarin, mun ruwaito cewa kamfanin man fetur na Najeriya, NNPC ya fara shirin karbo sabon bashin $2bn da zai bashi damar tafiyar da ayyukansa.

Shugaban kamfanin, Mele Kyari ya bayyana hakan a yayin da rahotanni suka bayyana cewa NNPC na fuskantar matsin lamba sakamakon wahalar fetur ta tsananta.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.