A Karshe: Tinubu Ya Yarda Akwai Yunwa a Najeriya, Ya Dauki Sabon Mataki

A Karshe: Tinubu Ya Yarda Akwai Yunwa a Najeriya, Ya Dauki Sabon Mataki

  • Gwamnatin tarayya ta tabbatar da cewa yunwa ta yi katutu ga al'ummar Najeriya saboda matsaloli mabanbanta
  • Biyo bayan haka, gwamantin ta kafa sabon kwamitin yaki da yunwa da zai tabbatar da abinci ya wadata a Najeriya
  • Mambobin kwamitin sun fara bayyana matakin da za su dauka domin ganin an yaki yunwa da samar da abinci a fadin Najeriya

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.

FCT Abuja - Gwamnatin tarayya ta bayyana dauki matakin gaggawa bayan amincewa akwai yunwa a Najeriya.

A yau juma'a, 12 ga watan Yuli mataimakin shugaban kasa, Sanata Kashim Shettima ya kaddamar da kwamitin a fadar shugaban kasa.

Kashim Shettima
Gwamnati ta kafa kwamitin yaki da yunwa. Hoto: Kashim Shettima.
Asali: Facebook

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa gwamnatin ta tattatauna da wasu gwamnonin jihohi da masana kan yadda za a samu mafita.

Kara karanta wannan

Ana shirin zanga zanga, gwamnati ta dauki matakin gaggawa domin samar da abinci

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Shettima: 'Akwai yunwa a Najeriya'

Mataimakin shugaban kasa ya tabbatar da cewa a yanzu ba za a cigaba da musu kan cewa akwai yunwa a Najeriya ko babu ba.

Kashim Shettima ya ce dole ne a yarda cewa Najeriya na fama da matsalar abinci domin a fara neman mafita.

Aikin kwamitin yaki da yunwa

Yayin da yake jawabi, Sanata Kashim Shettima ya ce ba a kafa kwamitin domin ya zama kishiya ga ma'aikatar noma ba.

Ya ce kwamitin zai yi aikin gaggawa ne domin ganin an magance matsalolin abinci kawai a Najeriya, rahoton the Guardian.

Yan kwamiti sun bayar da shawara

Gwamnonin da ke cikin kwamitin sun tabbatarwa gwamnati cewa akwai bukatar sake duba yadda ake noma a Najeriya.

Gwamna Babagana Umara Zulum ya ce an kara yawa sosai a Najeriya kuma ba a noman da za ta ciyar da mutane saboda haka ya kamata a shigo da tsarin zamani a harkar noma.

Kara karanta wannan

Ana murnar janye haraji, gwamnati ta gindaya sharadi kan farashin kaya

Za a bunkasa noma a Najeriya

A wani rahoton, kun ji cewa gwamnatin tarayya ta dauki sabon mataki kan bunkasa harkokin noma domin samar da wadataccen abinci a fadin Najeriya.

A sabon yunkurin, gwamantin shugaba Asiwaju Bola Ahmed Tinubu za ta samar da motocin noma da dama da wasu kayayyaki.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ibrahim Yusuf avatar

Ibrahim Yusuf (Hausa Editor) Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum. ibrahim.yusuf@corp.legit.ng