Tumatur Ya Yi Tsada a Najeriya, Manoma Sun Fadi Abin da Ya Sa Jar Miya Ta Gagara

Tumatur Ya Yi Tsada a Najeriya, Manoma Sun Fadi Abin da Ya Sa Jar Miya Ta Gagara

  • A yayin da mafi yawan kayan masarufi suke kara tsada a Najeriya, kayan miya sun shiga sahun abubuwan da suka kara kudi
  • A gefe guda, farashin danyen tumatur ya yi tashin gauron zabi tare da wahalar samuwa a mafi yawan kasuwannin Najeriya
  • Legit ta tattauna da mai noman tumatur a garin Kwadon da ke jihar Gombe domin jin yadda nomar rani ta gudana a yankin su

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.

Jihar Bauchi - Tsare-tsaren da gwamnatin tarayya ta fitar na cigaba da kawo tsadar kayan masarufi a kasuwannin Najeriya.

A kwanan nan an fara samun tsadar kayan miya a bangarori da dama na Arewaci da kudancin Najeriya.

Kara karanta wannan

Kananan hukumomi: Tinubu ya bayyana dalilin kai gwamnonin jihohi 36 kotu

Tsadar tumatur
Manoma sun ce karin kudin mai ya jawo tashin farashin tumatur. Hoto: Hassan Bahaushe Gombe
Asali: Facebook

Wasu manoma a jihar Bauchi sun bayyanawa jaridar Daily Trust dalilan da suka jawo karanci da tsadar tumatur a Najeriya.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Dalilin tsadar tumatur a Najeriya

Masu nomar rani a jihar Bauchi sun bayyana cewa karin kudin mai da kudin wuta suna cikin abubuwan da suka hana mutane da dama noman rani a Najeriya.

Sun ce rashin nomar yadda ya kamata ya haifar da ƙarancin tumatur a kasuwanni wanda ya jawo tsadarsa sosai.

Karin haske daga shugaban manoma

Shugaban masu noman rani a jihar Bauchi, Alhaji Sani Abubakar ya ce dole farashin ya cigaba da tashi saboda matsaloli da dama.

Ya ce matuƙar ba a samo mafita ga abubuwan da suka jawo tashin farashin ba to dole zai cigaba da haurawa a kowace rana.

Yadda farashin kayan miya ya tashi

Kara karanta wannan

'Daɗi zai biyo baya' Masana sun fadi dalilin goyon bayan tsare tsaren Tinubu

Shugaban manoman ya bayyana cewa tashin farashin ya shafi dukkan kayan miya da ake nomawa a rani.

A cewarsa, a bara sun sayar da buhun tattasai a N2,500 amma a yau saboda matsalolin tattalin arziki suna sayar da shi a N60,000 zuwa N80,000.

Legit ta tattauna da mai nomar rani

Legit ta tattauna da wani manomi a garin Kwadon, Usman Muhammad domin jin yadda nomar rani ta gudana a yankin su.

Usman ya tabbatarwa Legit cewa tsadar man fetur ta shafi nomar rani a Kwadon ta inda manoma da yawa sun ajiye noma a wannar shekarar.

Dalilin karin kudin wutar lantarki

A wani rahoton, kun ji cewa gwamnatin tarayya, ta ce ta janye tallafin wutar lantarki ne domin wadatar da wutar a Nijeriya nan da shekara uku masu zuwa.

Ministan makamashi, Adebayo Adelabu ya bayyana hakan a Abuja, inda ya ce dole 'yan Najeriya za su biyan kudin wuta da tsada.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ibrahim Yusuf avatar

Ibrahim Yusuf (Hausa Editor) Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum. ibrahim.yusuf@corp.legit.ng