"Yan Ta'adda na Barna a Tituna Fiye da Rashin Kyawun Hanyoyi," Shugaban Jami'a

"Yan Ta'adda na Barna a Tituna Fiye da Rashin Kyawun Hanyoyi," Shugaban Jami'a

  • An gano yadda yan ta'adda da ayyukansu ke mummunar barazana daga rayukan 'yan Najeriya musamman matafiya
  • Shugaban jami'ar kimiyya da fasaha ta jihar Enugu, Farfesa Aloysius Michaels Okolie ne ya shaidawa hukumar kare afkuwar hadurra matsalar
  • Ya ce yanzu haka ta'addanci, ciki har da garkuwa da mutane da fashi da makami sun fi salwantar da rayukan 'yan kasa

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

Jihar Enugu - Shugaban jami'ar kimiyya da fasaha ta Enugu, Farfesa Aloysius Michaels Okolie ya gano abin da ya fi kashe 'yan Najeriya tsakanin 'yan ta'adda da rashin kyawun hanyoyi. Farfesa Okolie ya ce a yanzu haka, 'yan ta'adda sun fi lalatattun hanyoyin kasar nan kashe mutane.

Kara karanta wannan

An kama jagora a PDP, Atiku Abubakar ya zargi 'yan sanda da cin zarafin 'yan kasa

FRSC Oyo
Shugaban jami'a a Enugu ya ce 'yan ta'adda na salwantar da rayuka a titunan kasar nan Hoto: Federal Road Safety Corps
Asali: Facebook

Vanguard News ta tattaro cewa shugaban ya fadi haka ne lokacin da aka gabatarwa da jami'arsa sabon shugaban hukumar kare afkuwar hadurra yankin Ozalla.

"Garkuwa da mutane ya ta'azzara," Okolie

Shugaban jami'ar kimiyya da fasaha ta jihar Enugu, Farfesa Aloysius Michaels ya Okolie ya koka kan ta'azzarar ayyukan rashin tsaro a titunan Najeriya.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ya bayyana haka ne a karshen mako, inda ya ce dawowar garkuwa da mutane da fashi da makami sun fi hallaka 'yan kasar nan kan munanan hanyoyin da ake da su.

Shugaban ya koka kan ƙaruwar kuncin rayuwa tsakanin 'yan kasa, wanda ke taka rawa wajen gudun wuce sa'a a tituna.

Ya ce matsin tattalin arziki a Najeriya babbar barazana ce ga rayuwar talakawan Najeriya, kuma rashin tsaro da munanan tituna na kara ta'azzara lamarin.

Kara karanta wannan

Aliko Dangote ya bayyana tsawon lokacin da za a dauka wajen farfado da tattalin arziki

Farfesa Okolie ya yi alkawarin bayar da hadin kai ga hukumar FRSC wajen dakile yawaitar hadurra a yankin.

An sace fasto a hanyar zuwa jana'iza

A baya mun ruwaito cewa 'yan ta'adda sun sace wani malamin addinin musulunci a hanyarsa ta zuwa jihar Legas domin binne mahaifiyarsa.

Rahotanni sun bayyana cewa 'yan bindiga sun kai hari kan motar da malamin addinin kiristan ke ciki tare da sace dukkanin fasinjojin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano.