Sojoji Sun Ragargaji 'Yan Bindiga a Jihohi, Sun Kama Manyan 'Yan Ta’adda

Sojoji Sun Ragargaji 'Yan Bindiga a Jihohi, Sun Kama Manyan 'Yan Ta’adda

  • Rundunar sojin Najeriya ta kai farmaki kan taron manyan yan ta'adda a jihohin Imo da Kwara domin dakile ayyukan barna
  • Farmakin ya ba sojojin Najeriya nasarar cafke wasu manyan yan ta'addan da suka fitini al'umma da ayyukan ta'addanci
  • Har ila yau, rundunar sojin ta bayyana irin makaman da ta kwace wajen yan ta'addar a yayin farmakin da ta kai a kansu

Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.

Imo, Kwara - Rundunar sojin Najeriya ta kai farmaki kan yan ta'adda a jihohin Imo da Kwara.

Farmakin na cikin kokarin da sojojin Najeriya ke yi domin yaki da ta'addanci da tayar da kayar baya.

Kara karanta wannan

Harin bam: Rundunar sojojin Najeriya ta fadi yadda za ta yi da 'yan ta'adda

Sojojiin Najeriya
Sojoji sun yi nasara kan yan ta'adda a jihohi. Hoto: HQ Nigerian Army
Asali: Getty Images

Legit gano haka ne a cikin wani sako da rundunar sojin Najeriya ta wallafa a shafinta na Facebook.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sojoji sun kama yan ta'adda a Imo

Sojin Najeriya sun kai farmaki kan ƴan ta'addar IPOB a karamar hukumar Orlu a jihar Imo inda suka kama wasu daga cikin manyan yan kungiyar.

Daga cikin wadanda aka kama akwai Izuchukwu Emejuru, Chibozor Chikwe tare da kwato bindigogin zamani da na gargajiya a tattare da su.

Sojoji sun kama yan ta'adda a Onuimo

Haka zalika, rundunar sojin ta kai samame a karamar hukumar Onuimo a jihar ta Imo inda ta kama wani dan kungiyar IPOB da ake kira da Bam Bam.

Rundunar ta kuma kai wani farmaki kan yan ta'addar IPOB a karamar hukumar Okigwe a jihar Imo inda ta fatattakesu tare da kwato makamai.

Kara karanta wannan

Bayan tashin bama-bamai a Borno, sojoji sun kashe 'yan ta'adda har maboyarsu

'Dan ta'adda ya fada hannun sojoji a Kwara

A wani farmaki da rundunar sojin Najeriya ta kai ƙaramar hukumar Edu a Kwara, ta kama wani dan bindiga mai suna Ibrahim Abdullahi.

Ana zargin Ibrahim Abdullahi da ayyukan ta'addanci a jihar kuma an kwato bindigogi da sauran makamai a hannunsa.

Sojoji sun kama masu leken asiri

A wani rahoton, kun ji cewa sojoji sun kama wasu mata uku masu tallar zuma a bakin titin bisa zargin yiwa ƴan bindiga leƙen asiri a jihar Kaduna.

Rahotanni sun nuna cewa an kama waɗanda ake zargin ne a kusa da kauyen Dogon Daji da ke ƙaramar hukumar Kagarko.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ibrahim Yusuf avatar

Ibrahim Yusuf (Hausa Editor) Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum. ibrahim.yusuf@corp.legit.ng

Online view pixel