"Kul Fa": Cibiyar Shari'ar Musulunci Ta Yi Gargadi Mai Tsauri Kan Taɓa Kimar Sultan

"Kul Fa": Cibiyar Shari'ar Musulunci Ta Yi Gargadi Mai Tsauri Kan Taɓa Kimar Sultan

  • Yayin da ake ci gaba da dambarwa kan taba ikon Sarkin Musulmi, an gargadi gwamnatin Sokoto kan shigar da siyasa
  • Cibiyar dabbaka shari'ar Musulunci ta gargadi gwamnatin jihar kan wasa da iko da kuma darajar da Sultan ke da shi a Najeriya
  • Hakan ya biyo bayan zargin rage ikon Sultan bayan kirkirar sabuwar doka da Majalisar jihar ta yi wanda jama'a da dama suka kushe

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Sokoto - Cibiyar dabbaka shari'ar Musulunci ta gargadi gwamnatin jihar Sokoto kan wasa da rawanin Sarkin Musulmi.

Cibiyar ta tura gargadin ne yayin da ake zargin Majalisar jihar ta tabbatar da wata doka da zata rage ikon Sultan kan nadin hakimai.

Kara karanta wannan

Gwamnati ta dauki mataki kan basarake da kansilan APC da suka sace randar wutar lantarki

An gargadi gwamnatin Sokoto kan taba martabar Sultan
Cibiyar shari'ar Musulunci ta gargadi gwamnan Sokoto kan taba darajar Sultan. Hoto:@ahmedaliyuskt.
Asali: Twitter

Sultan: An gargadi gwamnatin Sokoto

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da shugaban cibiyar, Aliyu Ibrahim Altukri ya fitar, cewar Daily Trust.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Altukri ya ce suna daga cikin masu ruwa da tsaki a Majalisar Sultan inda suka ja kunnen gwamnatin kan saka siyasa a lamarin.

Cibiyar ta ce Sultan ba wata hukuma ba ce a cikin gwamnatin Sokoto illa wani mukami ne mai daraja da Musulman Najeriya ke mutuntawa, Daily Post ta tattaro.

"Muna daga cikin masu ruwa da tsaki a Majalisar Sultan kuma muna Allah wadai da wani yunkuri na shigar da siyasa kan lamarin."

- Ibrahim Alkutri

Dokar rage ikon Sultan kan nadin hakimai

Wannan na zuwa ne yayin da Majalisar jihar ta kirkiri wata doka kan nadin hakimai a jihar.

A baya, Majalisar Sultan na da ikon nada hakimai ba tare da sanin gwamnatin jihar ba amma wannan doka ta sauya tsarin.

Kara karanta wannan

Gwamnatin Sokoto ta fadi abin da zai hana dawo da hakiman da aka tsige duk da umurnin kotu

A yanzu, Majalisar Sultan ba ta da ikon nadin hakimai ba tare da sahalewar gwamnatin jihar ba.

Sokoto: Kotu ta haramta dokar tsige hakimai

Kun ji cewa A zaman Majalisar jihar Sokoto na ranar Talata, an ruwaito cewa kudurin da zai yi gyara ga dokar masarautar ya tsallake karatu na farko da na biyu.

A sabuwar dokar za ta rage karfin ikon Mai alfarma Sa'ad Abubakar III, wanda ya haɗa da cire ikon naɗa hakimai ko masu naɗin sarki ba tare da izinin gwamnatin ba.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.

Online view pixel