Hotonan Yadda Aka Gudanar da Liyafar Murnan Dawowar Sarki Sanusi II a Kano

Hotonan Yadda Aka Gudanar da Liyafar Murnan Dawowar Sarki Sanusi II a Kano

  • Yayin da Gwamna Abba Kabri ya mayar da Muhammdu Sanusi II kujerar sarauta, wasu kungiyoyi sun nuna farin ciki
  • Kungiyoyin da suka yi liyafar sun hada da kungiyar Muhammadu Sanusi II colloquium da 'Yan Dangwalen jihar Kano
  • Kungiyoyin sun bada gudnmawa sosai wurin kiran Gwamna Abba Kabir ya dawo da Sanusi II bayan hawa mulkin jihar

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Kano - Wasu magoya bayan Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II sun gudanar da liyafa ta musamman a jihar.

'Yan a mutun Sarkin sun taru ne domin nuna jin dadinsu bayan mayar da Sanusi II kan kujerar sarautar jihar.

Hotunanliyafar murnan dawowar anusi II kujerar sarautar Kano
An gudanar da liyafar murnan dawowar Sanusi II sarautar Kano. Hoto: 'Yan Dangwalen jihar Kano.
Asali: Facebook

Sanusi II: An gudanar da liyafar murna

Kara karanta wannan

Sarautar Kano: Abin da Sanusi II ya fadawa kungiyar mata masu tafsiri a fadarsa

Magoya bayan sun hada da kungiyar Muhammadu Sanusi II colloquium da 'Yan Dangwalen jihar Kano, cewar Daily Trust.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Kungiyoyin na daga cikin wadanda suka yi ta kiran mayar da Sanusi II kan kujerar tun bayan nasarar Gwamna Abba Kabir.

Ganawar ta musamman an yi ne domin nuna jin dadi da kuma godiya ga Allah game da dawowar Muhammadu Sanusi II.

Shugaban liyafar, Ibrahim Musa Abubakar da aka fi sani da Sanyi-Sanyi ya ce musabbabin taruwar shi ne taya Sanusi II murna.

"Ba za mu iya nuna jin dadinmu kan wannan lamari na dawo da Sanusi II kujerar sarautar jihar Kano ba."
"Wannan shi ne dalilin haduwarmu a yau domin yin godiya ga ubangiji da kuma murnan abin da ya faru a Kano."

- Cewar Sanyi-sanyi

Liyafar ta samu halartar manyan mutane da mukarraban gwamnati da sauran al'umma magoya bayan Sanusi II.

Kara karanta wannan

Bidiyo: Muhammadu Sanusi II ya gana da fitaccen malamin Musulunci a fadar Sarkin Kano

Kalli wasu daga cikin hotunan liyafar:

Liyafa
Liyafa
liyafa
liyafa
liyafa
liyafa

Sanusi II ya ba dattijo kyautar N200,000

A wani labarin, kun ji cewa Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II ya taimakawa wani dattijo bayan ya nemi taimako kan iftila'i a gidansa.

Dattijon ya bukaci taimako ne bayan wani bangare na gidansa ya rushe saboda mamakon ruwan sama da aka yi a jihar Kano.

Sanusi II ya gwangwaje dattijon da kyautar har N200,000 domin ya yi amfani da shi wurin gyaran bangaren da ya rushe.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.

Online view pixel