Ana Tsaka da Ricikin Siyasa: Gwamnan PDP Ya Rantsar da Sababbin Ciyamomi 23 a Jiharsa

Ana Tsaka da Ricikin Siyasa: Gwamnan PDP Ya Rantsar da Sababbin Ciyamomi 23 a Jiharsa

  • Gwamna Siminialayi Fubara na Ribas, ya rantsar da sababbin shugabannin kwamitocin riko na kananan hukumomi 23 na jihar
  • An gudanar da bikin rantsuwar ne a gidan gwamnatin jihar dake Fatakwal, babban birnin jihar a safiyar Laraba
  • Wannan na zuwa ne bayan da gwamnan ya aike da sunayen shugabannin rikon zuwa majalisar jihar domin tantance su

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Fatakwal, Jihar Ribas - Gwamnan jihar Ribas, Siminalayi Fubara, ya rantsar da sababbin shugabannin riko na kananan hukumomi 23 na jihar.

An yi bikin rantsuwar ne a ranar Laraba a gidan gwamnati da ke Fatakwal, babban birnin jihar cikin tsauraran matakan tsaro.

Fubara ya rantsar da sababbin shugabannin riko na jihar Ribas
Ribas: Fubara ya rantsar da ciyamomi 23 na jiharsa. Hoto: @SimFubaraKSC
Source: Facebook

Majalisar Ribas ta tantance ciyamomi 23

Kara karanta wannan

Sanusi II ya yi hawa: 'Yan sanda sun yi magana kan yadda aka yi Sallar Idi a Kano

Gidan talabijin na Channels ya rawaito cewa an gudanar da bikin ne a zauren majalisar zartarwar jihar inda kashin farko na shugabannin rikon su 11 suka karbi rantsuwa.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Hakan na zuwa ne kwana guda bayan Fubara ya mika jerin sunayen ga majalisar dokokin jihar karkashin jagorancin kakakin majalisar, Victor Jumbo.

‘Yan majalisar dai sun gayyaci wadanda aka mika sunayensu domin tantance su da misalin karfe 8:00 na safiyar Laraba, inji rahoton Vanguard.

Jerin sunayen ciyamomin da aka rantsar

Duba sunayen shugabannin riko 23 da Fubara ya rantsar da su a kasa:

Sunan ciyaman

Karamar hukuma

1

Madigai Dickson

Abua/Odua

2

Happy Benneth

Ahoada ta Gabas

3

Mr. Daddy John Green

Ahoada ta Yamma

4

Otonye Briggs

Akuku Toru

5

Reginald Ekaan

Andoni

6

Orolosoma Amachree

Asari Toru

7

Alabota Anengi Barasua

Bonny

8

Anthony Soberekon

Degema

9

Brain Gokpa

Eleme

10

David Omereji

Emouha

11

John Otamiri

Etche

12

Kenneth Kpeden

Gokana

13

Darlington Orji

Ikwerre

14

Marvin Yobana

Khana

15

Chijioke Ihunwo

Obia/Akpor

16

Princewill Ejekwe

Ogba/Egbema/Ndoni

17

Evans Bipi

Ogu/Bolo

18

Princess Ogan

Okrika

19

Promise Reginald

Omuma

20

Enyiada Cookey-Gam

Opobo/Nkoro

21

Gogo Philip

Oyigbo

22

Ichemati Ezebunwo

Port Harcourt

23

Matthew Dike

Tai

Kara karanta wannan

Rayuwar Tinubu za ta iya shiga hadari, majalisa ta nemi a siya masa sabon jirgi

Obasanjo ya magantu kan nasarar gwamnatinsa

A wani labarin, mun ruwaito Olusegun Obasanjo ya bugi kirji da cewa gwamnatinsa na daga cikin mafi nagarta wajen gudanar da mulki a tarihin Najeriya.

Olusegun Obasanjo ya ce gwamnatinsa na daga cikin mafi nagarta wajen gudanar da mulki a tarihi, wanda ta taimakawa dimokuraɗiyyar kasar na shekaru 25.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com