Aiki da Cikawa: Ana Tsaka da Bikin Babbar Sallah, Sojoji Sun Kashe Dan Bindigan da Ya Addabi Kaduna

Aiki da Cikawa: Ana Tsaka da Bikin Babbar Sallah, Sojoji Sun Kashe Dan Bindigan da Ya Addabi Kaduna

  • Sojoji a jihar Kaduna sun yi nasarar hallaka wani kasurgumin dan ta’adda mai alaka da Buharin Yadi a ranar Sallah
  • Rahoto ya bayyana kayayyakin da aka kwato a tattare da kasurgumin dan ta’addan da aka kasha a karamar hukumar Giwa
  • Sojojin Najeriya sun bayyana aniyarsu na tabbatar da ci gaba da wanzar da zaman lafiya a yankuna daban-daban na kasar

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Salisu Ibrahim ne babban editan sashen Hausa na Legit. Kwararren marubucin fasaha, harkar kudi da al'amuran yau da kullum ne, yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru takwas

Jihar Kaduna - Bayan kusan mako guda da kashe daya daga cikin kasurguman ‘yan ta’adda a Arewa maso Yamma, Buharin Yadi, da dakarun 1 Division suka yi, sojoji sun ga bayan daya daga cikin abokan barnarsa, Daushe.

Kara karanta wannan

Ana bikin sallah, 'yan bindiga sun tafka kazamar ta'asa a Sokoto, sun sheke mutum 10

An sheke Daushe ne a ranar babbar sallah, Lahadi, 16 ga Yuni, lokacin da sojoji suka kaddamar da farmaki kan ‘yan ta’adda a karamar hukumar Giwa a jihar Kaduna.

An hallaka shugaban 'yan bindiga a Kaduna
Yadda aka kashe kasurgumin dan bindiga a jihar Kaduna
Asali: Original

Domin cimma nasarar aikinsu na tabbatar da tsaro, an tura undunar sojoji zuwa yankin Sabon Layi, inda suka kutsa har yankin Kidandan.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sojoji na aikin tabbatar da tsaro a bikin sallah

Yayin da suka kusanci Kidandan, sojojin suka hango dan ta'addan yana tuka babur dinsa da gudu a kokarinsa na tserewa daga idon sojojin, kamar yadda kafar labarai ta Zagazola Makama ta ruwaito.

Nan take sojoji suka bi shi a guje har ta kai gay a jefar da babur din ya shilla a guje zuwa wani yankin da sojoji suka tarfa shi suka sheke.

A halin da ake ciki, sojoji na ci gaba da aiki don tabbatar da tsaro da kwanciyar hankali a jihohin Najeriya yayin da ake ci gaba da bikin sallah.

Kara karanta wannan

Sanusi II ya yi hawa: 'Yan sanda sun yi magana kan yadda aka yi Sallar Idi a Kano

‘Yan bindiga sun yi ta’asa a jihar Sokoto

A wani labarin, rahotannin da ke fitowa na cewa da safiyar Lahadi, 16 ga Yuni, wasu 'yan bindiga sun kai hari wani kauye a jihar Sokoto.

An rahoto cewa, tsagerun sun kashe mutane da yawa kuma sun sace wasu a lokacin wannan harin.

An samu labarin cewa maharam sun farmaki kauyen Dudun Doki a karamar hukumar Gwadabawa ta jihar Sakkwato, inda suka kashe mutane fiye da goma kuma suka sace mutane da yawa a wajen karfe 1.30 na dare, rahoton Vanguard.

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and is AfricaCheck's ambassador. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by prestigious newspapers like Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. He rose from Hausa Editor to Head of Desk at Legit. His commitment to excellence has earned him recognition, including the 2021 Best Hausa Editor award and the Legit Fearless Team Player of the Year 2023.

Online view pixel