Tinubu Ya Bukaci Daraktan Hukuma Dan Arewa da Buhari Ya Nada Ya Yi Murabus
- Shugaba Bola Tinubu ya bukaci Mista Mamman Ahmadu wanda ke jagorancin hukumar BPP ya yi murabus
- Tinubu ya ce hakan na daga cikin himmatuwarsa wurin ingantawa da kuma fadada ayyukan hukumar
- Hadimin shugaban a bangaren yada labarai, Ajuri Ngelale shi ya tabbatar da haka a cikin wata sanarwa da ya fitar
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.
FCT, Abuja - Shugaban kasa, Bola Tinubu ya bukaci babban daraktan hukumar sa ido a harkokin saye-saye na gwamnati, BPP, Mamman Ahmadu ya yi murabus.
Tinubu ya bukaci hakan ne domin fadada ayyukan hukumar da kuma ingantata da kuma bin diddigi.

Asali: Twitter
Tinubu ya bukaci Ahmadu ya yi murabus
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da hadiminsa, Ajuri Ngelale ya fitar a yau Asabar 15 ga watan Yuni a shafinsa na Facebook.
Ngelale ya ce Tinubu ya umarci Mamman da ya mika dukkan kayayyakin da ke ofishinsa ga mafi girman matsayi a hukumar.
"Shugaba Tinubu ya mika godiya kan irin gudunmawa da Mista Ahmadu ya bayar inda ya ke masa fatan alheri a rayuwa."
- Ajuri Ngelale
Jim kadan bayan fitar da wannan sanarwa, Bola Tinubu ya maye gurbin Ahmadu da tsohon kwamishina a jihar Lagos, Ayodeji Ariyo Gbeleyi.
Buhari ya nada Ahmadu daraktan BPP
A watan Satumbar shekarar 2016, shugaban kasa na wancan lokaci, Muhammadu Buhari ya nada Mamman Ahmadu a matsayin babban daraktan hukumar BPP.
Buhari ya amince da nadin Ahmadu a hukumar duba da kwarewar da yake da shi na tsawon shekaru.
Sauran wadanda aka naɗa mukaman akwai Dakta Isa Ali Pantami a matsayin babban daraktan hukumar NITDA.

Kara karanta wannan
Sarautar Kano: Sanusi II ya fadi kokarin Abba Kabir bayan barnar da Ganduje ya tafka
Tinubu ya naɗa Nasiru Gawuna mukami
A wani labarin, kun ji cewa Shugaba Bola Tinubu ya nada Nasiru Yusuf Gawuna babban mukami a Jami'ar Bayero da ke jihar Kano.
Tinubu ya nada Gawuna muƙamin shugaban kwamitin gudanarwar na Jami'ar bayan sake yin garambawul a mukaman.
Sauran ƴan kwamitim da ke karkashin Gawuna sun hada da Abubakar Dauda da Nora Alo da Ibrahim Obanikoro da kuma Musa Abbas.
Asali: Legit.ng