Hajji 2024: Za a Fassara Huɗubar Arafah Zuwa Hausa da Wasu Harsuna 19 Na Duniya

Hajji 2024: Za a Fassara Huɗubar Arafah Zuwa Hausa da Wasu Harsuna 19 Na Duniya

  • Hukumar kula Masallatai masu alfarma a ƙasa mai tsarki ta ce za a fassara hudubar hawan Arfah zuwa harshen Hausa da wasu harsuna 19
  • Alhazai sama da miliyan 1.5 ne za su taru a filin Arafah ranar Asabar, 16 ga watan Yuni cikinsu har da Musulmi 65,000 daga Najeriya
  • Wannan rana tana da matuƙar muhimmanci da falala a addinin Musulunci kuma ana kiranta da ranar tuba

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Saudi Arabia - Rahotanni sun tabbatar da cewa za a fassara huɗubar hawan Arafah ta aikin hajjin bana 2024 zuwa harsuna 20 cikin har da harshen Hausa.

Ana sa ran aƙalla mutane biliyan ɗaya ne a faɗin duniya za su saurari huɗubar a Hausa da wasu harsuna 19.

Kara karanta wannan

InnalilLahi: Ana shirin babbar Sallah wasu mutum 19 sun mutu lokaci guda a Arewa

Alhazai a dutsen Arafah.
Za a fassara huɗubar Arafah ta bana 2024 zuwa harsuna 20 Hoto: Inside The Haramain
Asali: Twitter

Sama da mahajjata miliyan 1.5 daga sassan duniya ne ake sa ran za su taru a dutsen Arafah, wanda ya ƙunshi musulmin Najeriya 65,000.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Hukumar kula da manyan Masallatai biyu masu alfarma ce ta bayyana haka a shafinta na manhajar X wanda aka fi sani da Twitter.

Shugaban hukumar, Sheikh Abdulrahman bin Abdulaziz Al-Sudais, ya ce muhimman sakonnin da huɗubar ta ƙunsa sun haɗa da juriyar addini da zaman lafiya.

Ahmed Al-Hamidi, mataimakin shugaban sashin harsuna da fassara, ya ce fassarar ta yi daidai da tsare-tsaren hukumar na shekarar 2024.

Harsuna 20 da za a fasara huɗubar Arafah

Ya ce za a fassara huɗubar zuwa Faransanci, Turanci, Farisa, Urdu, Hausa, Rashanci, Turkish, Punjabi, Chinese, Malay, Swahili, Sipaniya da Fotigal.

Sauran harsunan sune Amhari, Jamus, Sweden, Italiyanci, Malayalam, Bosniya da kuma Filipino.

Kara karanta wannan

Gwamnati ta kirkiro shirin musamman ga matasa masu hidimar NYSC

Ya ce shafin Manarat Al-Haramain, tashoshi na Alqur’ani da Sunnar Annabi (SAaw) da gidajen rediyon FM guda 10 ne za su haska huɗubar kai tsaye.

Kaɗan daga falalar Arafah

Ranar hawan Arafah tana da matuƙar muhimmanci a wurin Musulmi. Ana kiran wannna rana da, "ranar tuba," saboda yadda Allah SWT ke gafartawa bayinsa matukar sun roƙe shi a ranar Arafah.

Haka nan kuma ranar tana da falala mai yawa saboda Fiyayyen Halitta Annabi Muhammad (SAW) ya yi huɗubar bankwana a dutsen Arafah.

Ranar Arafah dai na zuwa ne kwana ɗaya gabanin ranar Idin layya watau Babbar Sallah kuma ita ce rana ta biyu a aikin Hajji.

Saudiyya ta tsaurara matakan tsaro

Wani rahoto ya zo cewa Kasar Saudiyya ta sanar da kammala shirye-shiryen samar da isasshen tsaro domin kare mahajjata a yayin gudanar da Hajjin bana

Ministan harkokin cikin gida, Abdulaziz bin Saud ne ya tabbatar da haka yayin wani atisaye da jami'an tsaron kasar suka gudanar

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262

Online view pixel