Kotun Koli Ta Tanadi Hukunci a Shari'ar da Tinubu Yake Yi da Gwamnoni 36

Kotun Koli Ta Tanadi Hukunci a Shari'ar da Tinubu Yake Yi da Gwamnoni 36

  • Kotu ta dauki mataki game da shari'ar da ake yi tsakanin Gwamnatin Tarayya da kuma gwamnonin jihohi 36 a Najeriya
  • Kotun Koli ta tanadi hukunci kan shari'ar inda ta bukaci duka bangarorin su saurari ranar da za ta tuntube su
  • Wannan na zuwa ne bayan Gwamnatin Tarayya ta maka gwamnoni a gaban kotu kan dakile ƴancin ƙananan hukumomi a kasar

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

FCT, Abuja - Kotun Koli ta tanadi hukunci kan shari'ar Gwamnatin Tarayya da gwamnonin jihohi 36 a Najeriya.

Kotun ta dauki matakin ne a yau Alhamis 13 ga watan Yuni kan korafin da aka shigar da gwamnonin kan ƴancin ƙananan hukumomi a kasar.

Kara karanta wannan

Magana ta ƙare, babbar kotu ta yanke hukunci a shari'ar sarautar Kano

Kotun Koli ta yi hukunci a shari'ar Tinubu da gwamnoni 36
Kotun Koli ta tanadi hukunci a karar da Tinubu ya shigar da gwamnoni 36 a Najeriya. Hoto: @NGRPresident.
Asali: Twitter

Matsayar kotu a shari'ar Tinubu da gwamnoni

Mai Shari'a, Mohammed Lawal Garba wanda ya jagoranci alkalan guda bakwai ya ce za su byyana ranar yanke hukuncin karshe ga duka bangarorin, cewar The Nation.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Lawal Garba ya bayyana haka ne jim kadan bayan lauyoyin duka bangarorin sun gabatar da korafe-korafensu kan shari'ar, Vanguard ta tattaro.

Musabbabin ƙarar gwamnoni da Tinubu ya yi

Hakan ya biyo bayan maka gwamnoni 36 da ke Najeriya kan zargin tauye hakkin kananan hukumomi 774 da suke yi.

Daga bisani kotu ta ba gwamnoni 36 wa'adin mako daya da su yi martani kan zarginsu da ake yi.

Gwamnonin jihohi sun kalubalanci shari'ar inda suka bukaci babbar kotun da ya yi fatali da korafin Gwamnatin Tarayya a kansu.

Har ila yau, kotun ta umarci Ministan Shari'a ya yi martani cikin kwanaki biyu bayan karbar korafi daga gwamnonin.

Kara karanta wannan

"Duk da masu ja da ikon Allah, mun yiwa mutanen Kano aiki," Gwamna Abba gida gida

Gwamnatin Tarayya ta maka gwamnoni a kotu

A wani labarin, kun ji yadda Gwamnatin Bola Ahmed Tinubu ta maka gwamnonin jihohin Najeriya 36 zuwa Kotun Koli.

Matakin da aka dauka na shari’a kan gwamnoni 36 ya biyo bayan rashin da’a da ake zarginsu da aikatawa a harkokin gudanar da kananan hukumomi.

Babban lauyan Tarayya kuma Ministan shari’a, Prince Lateef Fagbemi, SAN, ya shigar da karar mai lamba: SC/CV/343/2024.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.

Online view pixel