Kano: Fitaccen Basarake Ya Magantu Kan Dawo da Sanusi II, Ya Tura Masa Sako Na Musamman

Kano: Fitaccen Basarake Ya Magantu Kan Dawo da Sanusi II, Ya Tura Masa Sako Na Musamman

  • Sarki Muhammadu Sanusi II yana ci gaba karbar sakwannin taya murna daga manyan sarakuna da ƴan siyasa
  • Sarkin Gwandu a jihar Kebbi, Manjo-janar Muhammad Ilyasu Bashir shi ma ya taya Sarkin murnan dawowa kujerar sarautar Kano
  • Sarkin ya ce tabbas wannan nadin ya yi dai-dai duba da kwarewa da kuma jajircewa irin na Muhammadu Sanusi II

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Kebbi - Sarkin Gwandu a jihar Kebbi, Manjo-janar Muhammad Ilyasu Bashir mai ya taya Sarki Muhammadu Sanusi II murna.

Ilyasu Bashir ya tura sakon murnan ne ga Sanusi II bayan dawowa kan kujerar sarautar Kano a kwanakin baya.

Kara karanta wannan

Kano: Abin da ƴaƴan Sheikh Dahiru Bauchi suka faɗawa Sanusi II bayan kai masa ziyara

Sarkin Gwandu ya tura sako ga Sanusi II a Kano
Sarkin Gwandu, Muhammad Ilyasu Bashir ya taya Muhammadu Sanusi II murnan dawowa kujerar sarautar Kano. Hoto:@opeyemtech.
Asali: Twitter

Sarkin Gwandu ya taya Sanusi II murna

Mai Martaba ya ce wannan ba karamin ci gaba ba ne duba da kwarewar Sarki Muhammadu Sanusi II, cewar Vanguard.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sarkin ya kuma roki Allah ya ba Sanusi II hikima da kwazo wurin gudanar da shugabanci ba tare da nuna wariya ba.

Har ila yau, sarkin ya bukaci al'umma da su zauna lafiya da juna yayin da ake rigimar sarauta a jihar.

Gwamna ya ji dadin maido Muhammadu Sanusi II

Har ila yau, Gwamna Siminalayi Fubara na jihar Rivers ya fara taya Sarki Muhammadu Sanusi II murnar dawowa kujerar sarautar Kano.

Fubara ya bayyana jin dadinsa kan wannan mataki na Gwamna Abba Kabir inda ya ce tabbas hakan zai kawo ci gaba a jihar ganin yadda al'umma ke goyon bayan matakin.

Gwamnan ya bayyana haka a ranar Alhamis 23 ga watan Mayu yayin da suke gudanar da wani babban taro a jihar tare da Sanusi II a birnin Port Harcourt da ke jihar Rivers.

Kara karanta wannan

Bidiyon dubban mutane da suka tari Sarkin Kano bayan Juma'a, ya aika sako a huduba

Ƴaƴan Dahiru Bauchi sun ziyarci Sanusi II

A wani labarin, kun ji cewa ƴaƴan Sheikh Dahiru Bauchi sun kawo ziyara fadar Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II a ranar Litinin.

Tawagar karkashin jagorancin Aminu Dahiru Bauchi ta kai ziyarar domin nuna goyon baya ga Sarkin tare da nuna jin dadinsu.

Wannan na zuwa ne bayan tube sarkin Kano na 15, Aminu Ado Bayero tare da mayar da Muhammadu Sanusi II kujerar.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.