“Na Karbi Kaddara”: Sarkin Gaya Ya Yi Magana Bayan Gwamnatin Kano Ta Tube Rawaninsa

“Na Karbi Kaddara”: Sarkin Gaya Ya Yi Magana Bayan Gwamnatin Kano Ta Tube Rawaninsa

  • Tsohon Sarkin Gaya, Alhaji Aliyu Ibrahim Abdulkadir, ya amince da tsige shi daga mukaminsa a matsayin “mukaddari daga Allah”
  • Jawabin na sa na zuwa ne biyo bayan soke dokar da a baya ta daukaka manyan sarakuna biyar ciki har da shi Alhaji Abdulkadir
  • Tsohon sarkin ya kuma ce ba zai kalubalanci matakin a kotu ba kuma idan aka ba shi wani mukamin zai karba da hannu biyu-biyu

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Gaya, jihar Kano - Tsohon Sarkin Gaya, Alhaji Aliyu Abdulkadir, daya daga cikin sarakuna 5 da gwamnatin Kano ta rusa masarautun su ya ce sun karbi wannan hakan a matsayin kaddara.

Kara karanta wannan

Sarkin Kano: Zanga zanga ta barke a fadar masarautar Gaya da majalisa ta rusa

Kano: Sarkin Gaya da aka tsige ya yi magana
Kano: Sarkin Gaya ya ce ya karbi sauke shi daga kan mulki a matsayin kaddara. Hoto: Umabis, EngrAbbaKYusif
Asali: Facebook

A ranar Alhamis, Gwamna Abba Yusuf ya kori dukkan sarakunan da Ganduje ya nada a 2019 da suka hada da Gaya, Karaye, Rano, Bichi da kuma sarkin Kano.

Sarkin Gaya ya dauki kaddara

Da yake mayar da martani kan matakin da gwamnan ya dauka a wata hira da BBC Hausa, Sarki Abdulkadir da aka tsige ya ce ba ya jin haushin kowa.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ya kara da cewa ba shi da wani shiri na kalubalantar matakin a kotu kuma idan har aka kira shi domin yin aiki a wani matsayi zai karba da hannu biyu-biyu.

"Tabbas duk wanda irin hakan ta same shi ba zai ji dadi ba, to amma Allah ne ya kawo ka, kuma shi ne wanda ya kawo karshenka a mukamin."

- A cewar Alhaji Aliyu Abdulkadir.

Zanga-zanga ta barke a Gaya

Kara karanta wannan

Sarki 2 a lokaci 1: Lauyoyin Kano sun fitar da jawabi ganin an jibge jami'an Sojoji

Tun da fari, mun ruwaito cewa zanga-zanga ta barke a karamar hukumar gaya kan rusa masarautar Gaya da gwamnatin jihar Kano ta yi.

Masu zanga-zangar sun yi kira ne ga Gwamna Abba Yusuf da ya mayar da sarakunan da ya tsige tare da tsige Muhammadu Sanusi daga kan kujerar Sarkin Kano.

Sabuwar zanga-zanga ta barke a Nasarawa

A wani labarin, mun ruwaito cewa sabuwar zanga-zanga ta mamaye karamar hukumar Nasara inda mutane ke nuna bacin rai kan matakin gwamnatin jihar na kin bin umarnin kotu.

Masu zanga-zangar sun nemi gwamnatin jihar Kano da ta bi umarnin babbar kotun tarayya na dakatar da aikwatar da dokar da rusa masarautun biyar na jihar.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.

Online view pixel