Ana Cikin Ɗimuwa Bayan Jirgi Daga Kaduna Zuwa Abuja Ya Carke a Daji, Sojoji Sun Ja Daga

Ana Cikin Ɗimuwa Bayan Jirgi Daga Kaduna Zuwa Abuja Ya Carke a Daji, Sojoji Sun Ja Daga

Fasinjoji sun shiga fargaba bayan jirgin kasa daga Kaduna zuwa Abuja ya samu matsala a tsakiyar daji a Jere

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Kaduna - An shiga ɗimuwa yayin da jirgin kasa makare da fasinjoji ya kauce hanya a cikin daji ana tsaka da tafiya a jihar Kaduna.

Jirgin da ya dauko fasinjoji daga Kaduna zuwa Abuja ya carke ne a Jere da ke kan hanyar Abuja da safiyar yau Lahadi 26 ga watan Mayu.

Jirgin kasa ya ci karo da matsala daga Kaduna zuwa Abuja
An fara gyara yayin da jirgin kasa ya carke a daji daga Kaduna zuwa Abuja. Hoto: Africom.
Asali: Facebook

Jirgin kasa ya baro Kaduna zuwa Abuja

Jirgin ya baro Kaduna ne da misalin karfe 8:05 na safe zuwa Abuja amma ya samu matsala bayan awa daya da fara tafiya, Daily Trust ta tattaro.

Kara karanta wannan

Tinubu zai kaddamar da jirgin kasan Abuja, ya yi albishir 1 ga yan Najeriya

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

An girke jami'an tsaro domin gudun abin da ka iya faruwa a cikin dajin musamman harin yan bindiga.

Leadership ta tabbatar cewa a yanzu haka ana kan gyara inda kusan tarago uku ne suka kauce hanya a jikin jirgin yayin da ake tafiya.

Duk da jirgin ya tsaya ne a yanki mai duwatsu, jami'an sojoji da yan sanda sun hallara domin ba da kariya.

Kaduna: Babu wata sanarwa daga hukumar NRC

Har yanzu babu wata sanarwa daga hukumar kula da jiragen kasa ta Najeriya (NRC) kan lamarin da ya faru a yankin Jere da ke jihar Kaduna.

Rahotanni sun tabbatar da cewa injiniyoyi suna kan gyara domin daidaita komai yayin da mutane suke cikin dar-dar kan abin ka iya faruwa a wurin.

Fasinjoji sun shiga fargaban ne ganin yadda jirgin ya ɓaci a tsakanin duwatsu inda suke tunanin komai zai iya faruwa.

Kara karanta wannan

Rundunar sojojin Najeriya ta fatattaki 'yan ta'adda, an kamo miyagu a Abuja da Oyo

Jirgin sama ya kauce hanya a Lagos

A wani labarin, kin ji cewa wani jirgin sama dauke da fasinjoji 52 ya gamu da tsautsayi bayan ya kauce hanya a jihar Lagos.

Jirgin, mallakin Xejet Airlines ya kauce hanya ne tare da fantsama cikin daji a cikin filin jirgin saman Lagos.

Jami'an Hukumar kula da jiragen saman ta FAAN sun yi gaggawar kai dauki wurin domin ceto fasinjoji daga halin da suke cikin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.

Online view pixel