Ana Murnar Dala Ta Karye a Kasuwa, Babban Banki CBN Ya Ɗauki Sababbin Matakai

Ana Murnar Dala Ta Karye a Kasuwa, Babban Banki CBN Ya Ɗauki Sababbin Matakai

  • Yayin da darajar Naira ke ƙaruwa a kasuwa, babban bankin ƙasa CBN ya yi wasu sababbin sauye-sauye domin inganta ayyukan ƴan canji
  • CBN ya umarci halastattun ƴan canaji su sabunta lasisin aiki kuma ya cire masu dokar ajiye wasu adadin kudi kafin a ba su lasisi
  • Daraktan sashen tsare-tsaren kuɗi na babban bankin, Haruna Mustafa ne ya bayyana haka a wata sanarwa a ranar Laraba

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja - Babban bankin Najeriya (CBN) ya umarci halastattun ƴan canji da ke kasuwancin hada-hadar kudi su sabunta lasisin aikinsu.

Hakan na kunshe ne a wata sanarwa da daraktan tsare-tsaren kudi na CBN, Haruna Mustafa, ya fitar ranar Laraba, 22 ga watan Mayu, 2024.

Kara karanta wannan

Majalisa ta tsige sarkin Kano Aminu Ado Bayero? Shugaban masu rinjaye ya yi bayani

Gwamnan CBN, Yemi Cardoso.
CBN ya umarci ƴan canji su sabunta lasisi aikinsu a Najeriya Hoto: Cenbank
Asali: Twitter

Bankin ya kuma bukaci duk wani ɗan canji ya tabbata ya cika sharuɗɗan nau'in lasisinsa daga nan zuwa watanni shida, kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

"Dukkan ƴan canji da masu tallata ƴan kasuwar hada-hadar kuɗi su cike buƙatar neman sabon lasisi na kowane mataki ko nau'in da ya kwanta masu a rai," in ji CBN.

Bankin CBN ya yi sababbin sauye-sauye

Har ila yau, babban bankin ƙasar nan ya yi wasu sauye-sauye a kundin dokoki da ƙa'idojin ayyukan ƴan canjin da aka amince da su.

Ɗaya daga cikin canje-canjen da bankin ya yi shi ne cire tilascin ajiye N200m ga masu lasisi mai daraja ta farko watau Tier-1.

Haka zalika babban bankin ya jingine ajiye N50m ga masu lasisi mai ƙima ta biyu, cewar rahoton Vanguard.

Kara karanta wannan

"Dalilin da ya sa Kwankwaso, Atiku da Peter Obi ba za su kai labari ba a zaɓen 2027"

CBN ya kuma janye kudin sabunta lasisi na shekara-shekara na N5m ga ƴan canji da ke matakin farko da kuma N1m ga ƴan mataki na biyu.

Sanarwar ta ce:

"Babban Bankin Najeriya (CBN) ya fitar da daftarin ka'idojin gudanar da ayyukan ƴan canji a Najeriya a watan Fabrairun 2024, domin jin ra'ayoyin masu ruwa da tsaki.
"Bayan kammala jin shawarwarin masu ruwa a tsaki, a yanzu CBN ya fitar da daftarin ƙa'idojin da aka amince da su domin sa ido kan ayyukan ƴan canji a Najeriya."

Naira ta ƙara daraja a kasuwa

A wani rahoton kuma, an ji kimar Naira ta ƙara sama a kasuwar hada-hadar gwamnati ranar Talata sa'o'i 24 bayan kuɗin Najeriya sun rikita Dalar Amurka.

Rahoton FMDQ mai sa ido kan hada-hadar kuɗi ya nuna cewa Naira ta tashi da N3.31 inda aka yi musayar kowace Dalar Amurka kan N1,465.68.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262

Online view pixel