Fitattun 'Yan Arewa Guda 5 da Bola Tinubu Ya ba Manyan Mukamai a Jami’o’i

Fitattun 'Yan Arewa Guda 5 da Bola Tinubu Ya ba Manyan Mukamai a Jami’o’i

  • A makon da ya wuce shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya nada mutane 555 a manyan makarantu 111 a fadin Najeriya
  • Mutanensu 555 za su rike shugabancin kwamitocin gudanarwa na jami'o'i da kwalejojin ilimi da fasaha da ke cikin kasar
  • Legit ta tattaro muku sunaye da takaitaccen tarihin fitattun yan Arewa 5 da suka samu shugabancin kwamitocin ko zama mambobi

Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.

Arewa - Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya nada yan Najeriya mutum 555 domin rike shugabancin kwamitocin manyan makarantu a Najeriya.

Mukmai a jami'o'i
Tinubu ya ba fitattun yan Arewa mukamai a jami'oi. Hoto: Hoto: Mahmud Aliyu Shinkafi, Asiwaju Bola Tinubu, Yayale Ahmed
Asali: Facebook

Mutanen sun hada da yan siyasa, masu sarautar gargajiya, ma'aikatan gwamnati, yan kasuwa da sauransu.

Kara karanta wannan

Goodluck Jonathan ya tsoma baki kan rigimar Ministan Tinubu da gwamnan PDP

Mai taimakawa shugaban kasa a harakar yada labarai, Bayo Onanuga ya wallafa sunayen mutanen a shafinsa na X.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Tinubu: 'Yan Arewa da aka ba muƙamai

1. Farfesa Attahiru Jega

Shugaban kasa ya nada Farfesa Attahiru Jega shugabancin kwamitin gudanarwa na jami'ar Usman Dan Fodiyo da ke Sokoto.

Farfesa jega
Farfesa Attahiru Jega. Hoto: Elder Solomon Harry
Asali: Facebook

An haifi Farfesa Jega a shekarar 1957 a jihar Kebbi, ya kuma yi karatu a jami'o'in ABU Zariya da BUK kano.

Jega ya yi aiki a jami'ar Bayero inda tun daga malanta sai da ya dawo mataimakin shugaban jami'ar. A shekarar 2010 tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan ya nada shi shugaban hukumar INEC.

2. Isa Yuguda

Bola Ahmed Tinubu ya nada Isa Yuguda a matsayin shugaban kwamitin gudanarwa na jami'ar NOUN da ke gudanar da karatu ta yanar gizo.

Isa Yuguda
Malam Isa Yuguda. Hoto: Isa Yuguda
Asali: Facebook

An haifi Isa Yuguda a shekarar 1956 a jihar Bauchi. Ya kuma yi karatu a jami'o'in ABU da Jos.

Kara karanta wannan

Sheikh Pantami ya aiko ta'aziyya yayin da aka rasa daya daga cikin dattawan Gombe

Isa Yuguda ya kasance gwamna a jihar Bauchi na shekaru takwas kuma Olusegun Obasanjo ya nada shi ministan sufuri a lokacin da ya ke shugaban kasa kuma gogaggen tsohon ma'ikacin banki ne.

3. Dakta Aliyu Tilde

Shugaban kasa ya nada Dakta Aliyu Tilde mamba a kwamitin gudanarwar jami'ar gwamantin tarayya da ke Dutsim-ma a jihar Katsina.

Aliyu Tilde
Dakta Aliyu Tilde. Hoto: Aliyu U. Tilde.
Asali: Facebook

Dakta Tilde ya fito daga jihar Bauchi kuma gogaggen marubuci ne da ya shafe shekaru yana rubuce-rubuce a jaridu dabam-dabam.

Ya kuma rike mukamai daban daban a Najeriya daga cikinsu akwai kwamishinan ilimi a jihar Bauchi.

4. Alhaji Mahmud Yayale Ahmed

Shugaba Bola Tinubu ya nada Alhaji Yayale Ahmed shugaban kwamitin gudanarwa a jami'ar Ahmadu Bello da ke Zariya.

Yayale Ahmed
Alhaji Yayale Ahmed. Hoto: Yayale Ahmed
Asali: Facebook

An haifi Yayale Ahmed a shekarar 1952 a jihar Bauchi. Ya kuma yi karatu a jami'ar ABU Zariya da jami'ar Abuja.

Ya rike manyan mukamai cikinsu akwai ministan tsaro da shugaban ma'aikatan gwamnatin tarayya a lokacin mulkin Obasanjo.

Kara karanta wannan

"Gwamnatin Bola Tinubu ta jefa Najeriya cikin tsaka mai wuya," Dattijon Arewa

5. Mahmud Aliyu Shinkafi

An ba Mahmud Aliyu Shinkafi mukamin shugaban kwamitin gudanarwa a jami'ar jihar Filato da ke birnin Jos.

Aliyu Shinkafi
Mahmud Aliyu Shinkafi. Hoto: Hafis Aliyu Shinkafi
Asali: Facebook

An haifi Mahmud Aliyu Shinkafi a shekarar 1960 a jihar Zamfara. Ya kuma zama gwamnan jihar jami'ar ANPP amma daga baya ya canza sheka.

Tinubu ya ba da sababbin mukamai

A wani rahoton, kun ji cewa shugaba Bola Tinubu ya yi sababbin nade-nade a manyan hukumomi biyu a ranar Juma'a 19 ga watan Afrilu a Abuja.

Shugaban ya nada Mista Mairiga Aliyu a matsayin shugaban kwamitin hukumar SEC sai Halima Kyari a matsayin shugaba hukumar NAICOM.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ibrahim Yusuf avatar

Ibrahim Yusuf (Hausa Editor) Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum. ibrahim.yusuf@corp.legit.ng

Online view pixel