Mummunar Gobara Ta Tashi a Babbar Kasuwar Arewa, ’Yan Kasuwa Sun Tafka Asara

Mummunar Gobara Ta Tashi a Babbar Kasuwar Arewa, ’Yan Kasuwa Sun Tafka Asara

  • Wata mummunar gobara ta tashi a babbar kasuwar jihar Kwara, inda 'yan kasuwa suka tafka asara mai yawa a gaban idanunsu
  • An ruwaito cewa akalla shaguna biyar ne suka kone kurmus yayin da har yanzu ba a gano musabbabin tashin gobarar ba
  • Gobarar ta tashi a daren ranar Talata, ta yi ta ci har zuwa lokacin da 'yan kwana kwana na tarayya da na jiha suka kawo dauki

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Jihar Kwara - Wata mummunar gobara da ta tashi a safiyar ranar Talata ta babbake shaguna da dama a babbar kasuwar Owode da ke Offa, jihar Kwara.

Gobara ta tashi a babbar kasuwar Offa, jihar Kwara.
Akalla shaguna biyar ne gobara ta babbake a kasuwar Offa da ke jihar Kwara. Hoto: @Fedfireng
Asali: Facebook

'Yan kwana kwana sun kashe gobarar

Kara karanta wannan

Abuja: Mummunar gobara ta tashi a gidan shugaban karamar hukuma

Wani bidiyo da jaridar The Nation ta gani ya nuna yadda gobarar ta rika cinye shaguna yayin da 'yan kasuwa suka gaza kashe ta.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

"Wannan wutar ta yi yawa. Ba na tsammani wutar lantarki ce ta haddasa ta. Watakila wasu ne ke yin girki wutar ta kama, domin ta yi yawa sosai."

- A cewar wani dan kasuwa da aka ji muryarsa a cikin bidiyon.

SaharaReporters ta ruwaito cewa cewa jami'an hukumar 'yan kwana kwana na tarayya da na jiha ne suka taru suka kashe wutar.

"Yan kasuwa sun tafka asara" - Majiya

Wata majiya ta shaida cewa akalla shaguna biyar ne gobarar ta lakume su.

Majiyar ta ce:

"Har yanzu hukumomi na kan tantance lamarin, amma dai a ganin ido na, shaguna biyar sun kone kurmus.
"Muna maganar duniyoyi na miliyoyin Naira ne aka yi asararsu a wannan gobarar, amma na san hukuma za ta fitar da bayani nan gaba."

Kara karanta wannan

APC ta dauki zafi kan sharrin da aka yi wa Matawalle, ta gargadi PDP a Zamfara

Gobara a garuruwan jihar Kwara

Wannan gobarar na zuwa ne kasa da watanni takwas da aka samu tashin gobara a wani gida da ke cikin garin, wadda ta lalata dukiyar N6.5m.

Jaridar The Punch ta ruwaito cewa gobarar ta tashi misalin karfe 1:05 na dare a Kowope da ke yankin Olorunkuse, a Offa.

Haka zalika, a watan Disamba, akalla shaguna 14 ne suka babbake a garin Tanke da ke karamar hukumar Ilorin ta Kudu da ke Kwara.

Gobara ta tashi a kasuwar Kaduna

A wani labarin kuma, Legit Hausa ta ruwaito cewa wata mummunar gobara ta tashi a kasuwar Panteka da ke jihar Kaduna.

An ruwaito cewa bangaren 'yan katako a kasuwar ne ya kama da wuta, lamarin da ya jawo aka yi asarar dukiya mai yawa.

Asali: Legit.ng

Online view pixel