Bidiyon Wani Bahaushe Da Ya Yanka Kek Da Wayar iPhone 12 Pro Max Ya Girgiza Intanet

Bidiyon Wani Bahaushe Da Ya Yanka Kek Da Wayar iPhone 12 Pro Max Ya Girgiza Intanet

  • Jama'a sun yi cece-kuce kan bidiyon wani matashi 'dan Arewa da ya yi amfani da wayar iPhone dinsa ta wani salo da ba a saba gani ba
  • Matashin, wanda ke bikin zagayowar ranar haihuwarsa, ya yi amfani da wayarsa iPhone 12 Pro Max wajen yanka kek dinsa
  • Yayin da mutane da dama suka cika da mamakin cewa ya yi amfani da tsadaddiyar waya maimakon wuka, wasu sun ga al'ajabin dalilinsa na yin haka

Aisha Musa ta shafe tsawon shekaru tana kawo labaran Hausa a bangaren siyasa, tsegumi da al’amura

Wani bidiyo da ya yadu na wani matashin Bahaushe da ya yanka kek dinsa da wayar iPhone 12 Pro Max ya haddasa cece-kuce a soshiyal midiya.

@iphone_boy1 ne ya wallafa bidiyon a dandalin TikTok sannan ya amsa sakonni daga mutanen da suka aike masa da sakon fatan alkhairi kan zagayowar ranar haihuwarsa, wanda hakan ke nuni ga kek din shagalin ne.

Kara karanta wannan

"Za su illata ni": Matashi ya koka da 'yan Nepa suka bar lantarkin tsawon kwanaki 5 a jere

A cikin bidiyon, @iphone_boy1 ya dulmiya wayar iPhone din a tsakiyan kek din don raba shi gida biyu, yayin da abokansa suka dunga kallo ba tare da sun ce uffan ba.

Matashi ya tashi kan mutane a soshiyal midiya
Matashi ya yanka kek da wayar iPhone Hoto: @iphone_boy1
Asali: TikTok

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Masu amfani da soshiyal midiya sun cika da mamakin cewa kek din zagayowar ranar haihuwarsa ne ya yanka da iPhone maimakon karamin wuka.

Kalli bidiyon a kasa:

Jama'a sun yi martani kan abin da matashin ya yi

aishausman969 ta ce:

"Wayar da mutane ke neman suna da shi ya kai kanka ka mayar da shi wuka sannu da kokari."

francisthomas77242455 ya ce:

"Kafin ya shirya wannan ranar kun san kwana nawa ya yi amfani da shi wajen tunanin tsawon shekarun da babu kudi kuna wajen."

Debbie ta ce:

"Suna yaudararku ne yana ta amfani da wayar wajen boye wukar da ke a daya hannun."

Kara karanta wannan

Daliban jami'a 4 sun lakadawa abokin karatunsu duka har ya mutu, ‘yan sanda sun dauki mataki

Khalifa ya ce:

"Ka duk masu cewa abubuwan malam bahaushe ya sha bamban, idan 'dan kudu 'dan uwanku ne ya yi za ku kira shi zolaya amma tunda 'dan Arewa ne ya yi ya zama wani abun daban, babu komai face kiyayya wawayen mutane."

Wani ya kashe abokiyar karatunsa kan iPhone

A wani labarin, mun ji cewa an kama wani matashi dan shekara 21 da ke karatu a jami’ar Adekunle Ajasin, Akungba (AAUA) Olubodun Sanni, bisa zargin kashe wata Mis Adekunle Adebisi Ifeoluwa.

An tsinci gawar Miss Adekunle a ranar 2 ga Fabrairu, 2024 a cikin wani gida mai daki daya da ta yi haya a wajen makarantar.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng