Yunwa: Kungiyar Kwadago Ta Dakatar da Zanga-Zangar Gama Gari, An Fadi Dalili

Yunwa: Kungiyar Kwadago Ta Dakatar da Zanga-Zangar Gama Gari, An Fadi Dalili

  • Kungiyar NLC ta yi bayanin dalilin da yasa ta sanar da dakatar da zanga-zangar kwanaki biyu da ta fara a ranar Talata
  • A cewar shugaban kungiyar kwadagon, an cimma makasudin gudanar da zanga-zangar ne a ranar farko, wanda shine dalilin dakatar da tattakin
  • A ranar Litinin ne gwamnatin tarayya ta gana da shugaban kungiyar kwadagon domin dakile zanga-zangar, amma taron ya tashi baran-baran

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Aisha Musa ta shafe tsawon shekaru tana kawo labaran Hausa a bangaren siyasa, tsegumi da al’amura

Abuja - Kungiyar Kwadago ta Najeriya (NLC) ta sanar da dakatar da zanga-zangar da ta shiga na kwanaki biyu a fadin kasar, domin nuna adawa da manufofin tattalin arzikin Shugaba Bola Tinubu.

A karshen taronsu na ranar Talata, 27 ga watan Fabrairu, kungiyar ta shaida wa manema labarai cewa an cimma manufar gudanar da zanga-zangar ne a ranar farko da fara ta, rahoton Channels TV.

Kara karanta wannan

Yan sanda sun dakatar da zanga-zangar NLC a Borno a kan wani dalili 1 tak

Kungiyar kwadago ta dakatar da zanga-zangar gama gari da ta fara
Yunwa: Kungiyar Kwadago Ta Dakatar da Zanga-Zangar Gama Gari, An Fadi Dalili Hoto: Nigeria Labour Congress
Asali: Twitter

Sanarwar da shugaban kungiyar ya fitar na cewa:

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

"Saboda haka, taron NEC ya yanke shawarar dakatar da zanga-zangar a rana ta biyu bayan da aka samu gagarumar nasara, don haka an cimma mahimman manufofin zanga-zangar na kwanaki 2 a ranar farko."

Kungiyar ta kuma yaba ma daukacin 'yan Najeriya, shugabanni da ma'aikata kan tururwa da suka yi a fadin kasar don yin zanga-zangar lumana kan halin da ake ciki, rahoton Nigerian Tribune.

An shirya zanga-zangar ne sakamakon cire tallafin man fetur wanda ya janyo hauhawar farashin kayan abinci, tabarbarewar tattalin arziki, hauhawar farashin kayayyaki da tsadar rayuwa a kasar.

Zanga-zanga: Gwamnan tarayya ta gana da NLC

Gwamnatin tarayya da Shugaban kasa Bola Tinubu ke jagoranta ta gana da shugabannin kwadago a daren Litinin, 26 ga watan Fabrairu, amma aka tashi baran-baran inda NLC ta ce lallai za ta yi zanga-zangar da ta shirya.

Kara karanta wannan

Hotunan yadda Kanawa suka karade titunan Kano a zanga-zangar kin jinin tsadar rayuwa

Daga nan sai NLC ta tsayar da harkokin tattalin arziki cak a ranar Talata domin yin zanga-zanga.

Shugaban kungiyar kwadagon, Joe Ajaero, ya ce zanga-zangar saboda yunwa da ke kasar ne ba wai don neman a duba karancin albashi ba.

'Yan sanda sun dakatar da zanga-zangar NLC a Borno

A wani labarin, mun ji cewa tawagar rundunar yaki da ta'addanci karkashin jagorancin kwamishinan 'yan sanda ta dakatar da zanga-zangar kungiyar kwadago ta Najeriya NLC a jihar Borno.

Zanga-zangar adawa da tsadar rayuwar an gudanar da ita ne a fadin kasar a ranar Talata, kuma an fara ta a Borno da karfe 8 na safe amma ‘yan sanda suka dakatar da ita.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng