Jerin Kasashen Nahiyar Afirka 10 da Aka Fi Dauke Wutar Lantarki da Yawan Daukewar a Shekara

Jerin Kasashen Nahiyar Afirka 10 da Aka Fi Dauke Wutar Lantarki da Yawan Daukewar a Shekara

Najeriya na daga cikin kasashen Nahiyar Afirka da suka fi fuskantar matsalar wutar lantarki a yankin.

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Tun shekaru da dama da suka wuce wutar ke cikin wani yanayi wanda har zuwa yanzu an gagara shawo kan matsalar.

Kasashen Nahiyar Afirka 10 da suka fi matsalar wutar lantarki
Kasashen da ke fama da matsalar wutar lantarki a Afirka. Hoto: Bola Tinubu, TRCN.
Asali: Facebook

Masana sun tabbatar da cewa wutar lantarki kusan ita ce hanyar farfado da tattalin arziki wanda idan babu za a iya samun matsala.

Legit Hausa ta jero muku kasashe 10 da aka fi yawan dauke wutar lantarki a Nahiyar Afirka da aka fitar daga 2014 zuwa 2022.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

1. Najeriya

Rahoton Cobiyar Utility Bidder a Burtaniya ya tabbatar da cewa a Najeriya ana dauke wutar har sau 394 a duk shekara.

Kara karanta wannan

Rayuka 7 sun salwanta saboda turmutsitsi a wajen siyan shinkafar kwastam a jihar APC

Wannan dauke wutar da ake yi a Najeriya shi ne mafi muni a Nahiyar a matsayinta na wacce ake yi wa lakabi da giwar Afirka.

2. Afirka ta Tsakiya

Wannan kasa da ke yankin Nahiyar Afirka ta Tsakiya da aka fi sani da Central African Republic ta kasance a mataki na biyu a jerin kasashen 10 inda ake daukewa sau 349.

3. Benin

Kasar Benin da ke makwabtaka da Najeriya ta kasance a mataki na uku inda ake dauke wutar sau 336 a cikin shekara daya.

4. Nijar

Kasar Nijar ita ma da ke makwabtaka da kasar Najeriya ta na fama da matsalar inda ake daukewa sau 264 a shekara.

5. Congo

Kasar Congo wacce ke jerin kasashe masu tasowa a Nahiyar ana dauke wutar sau 258 a shekara.

6. Gambia

Kasar da ake kira The Gambia ta kasance a mataki na shida inda ake dauke wutar sau 253 a cikin shekara, cewar Aminiya.

Kara karanta wannan

Gawarwaki sun fara rubewa a barikin soja bayan matakin da kamfanin wuta ya dauka, an fadi dalili

7. Burundi

Kasar na daga cikin kananan kasashe da ke fama da matsalar yayin da ake dauke wutar sau 199 a cikin shekara.

8. Zambia

Kasar da ke mataki na takwas na fuskantar matsalar wanda ya ke jawo matsalar tattalin arzikin kasar, ana dauke wutar sau 160.

9. DR Congo

Jamhuriyar Dimukradiyya ta Congo ta kasance a mataki na tara inda ake dauke wutar har sau 148 a shekara.

10. Burkina Faso

Kasar da ke mataki na 10 a cikin jerin kasashen ita ce Burkina Faso wacce ke hannun sojoji, ana dauke wutar sau 118 a cikin shekara guda.

Minista ya bukaci cire tallafin wuta

Kun ji cewa, Ministan Makamashi, Adebayo Adelabu ya ce gwamnati ba za ta iya ci gaba da biyan kudin tallafin wuta ba.

Adelabu ya ce akwai yiwuwar su cire tallafin wutar saboda basukan da kamfanonin ke bi.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.