Jam'iyyar PDP ta Dau Zafi Kan Sace Shugabanta, Ta Aike da Muhimmin Sako Ga Tinubu

Jam'iyyar PDP ta Dau Zafi Kan Sace Shugabanta, Ta Aike da Muhimmin Sako Ga Tinubu

  • Jam'iyyar PDP ta nuna takaicinta kan sace shugaban jam'iyyar da aka yi na jihar Legas kan hanyarsa ta dawowa daga tafiya
  • Jam'iyyar PDP cikin wata sanarwa da ta fitar ta yi Allah wadai da yadda sace-sacen mutane ke ƙara ƙaruwa a ƙasar nan a mulkin Tinubu
  • PDP ta buƙaci jami'an tsaro da su gaggauta ceto shugaban jam'iyyar daga hannun miyagun da suka yi garkuwa da shi

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

FCT, Abuja - Jam'iyyar PDP ta buƙaci a gaggauta sakin shugaban jam'iyyar reshen jihar Legas Hon. Philip Olabode Aivoji, wanda aka sace a hanyarsa ta zuwa Legas daga Ibadan, babban birnin jihar Oyo.

Hakan dai na ƙunshe a wata sanarwa da sakataren yaɗa labarai na jam'iyyar, Debo Ologunagba, ya fitar a ranar Asabar, 27 ga watan Janairu.

Kara karanta wannan

Abu ya girma: Ƴan bindigan da suka sace shugaban PDP na jiha sun aiko da saƙo mai ɗaga hankali

PDP ta yi martani kan sace shugabanta
Jam'iyyar PDP ta bukaci a gagguta sako shugabanta da aka sace a Legas Hoto: @OfficialPDPNig
Asali: Facebook

Jam'iyyar ta kuma yi Allah wadai kan yadda ake yawaitar samun sace-sacen mutane domin karɓar kuɗin fansa a ƙasar nan.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Jam'iyyar ta kuma yi kiran da a gaggauta sakin duk wasu waɗanda suke tsare a hannun masu garkuwa da mutane a faɗin ƙasar nan.

PDP ta nuna takaicinta kan yadda lamuran tsaro ke ƙara taɓarɓarewa a ƙasar nan a ƙarƙashin jagorancin Shugaba Tinubu, wanda ta ce har yanzu ya gaza yin wani kataɓus a kai.

Wane saƙo PDP ta aike da shi?

Wani ɓangare na sanarwar na cewa:

"PDP ta damu matuƙa kan lafiyar Honorabul Aivoji musamman la'akari da shekarunsa da yanayin lafiyarsa."
"Jam’iyyar PDP ta buƙaci jami’an tsaro da su ɗauki matakin gaggawa don ganin an sako Honorabul Aivoji da duk wasu ƴan Najeriya da suke tsare a sansanonin masu garkuwa da mutane a sassa daban-daban na ƙasar nan.

Kara karanta wannan

Tafiyar Tinubu zuwa Faransa ta bar baya da kura yayin da PDP da LP suka yi masa tonon silili

"Jam’iyyar mu na kira ga ƴan Najeriya da su kasance cikin shiri, su kuma ci gaba da ba jami’an tsaro goyon baya a kokarinsu na kare al’ummarmu a wannan mawuyacin lokaci."

PDP Ta Yi Martani Kan Tsige Kakakin Majalisar Ogun

A wani labarin kuma, kun ji cewa jam'iyyar PDP reshen jihar Ogun ta yi martani kan tsige kakakin majalisar dokokin jihar da ƴan majalisar suka yi.

Jam'iyyar ta bayyyana cewa matakin ya dace duba da yadda ake tuhumarsa da aikata almundahana mai tarin yawa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng