Betta: Gbajabiamila Ya Amince da N2bn Ba Tare da Izinin Tinubu Ba? Fadar Shugaban Kasa Ta Yi Martani

Betta: Gbajabiamila Ya Amince da N2bn Ba Tare da Izinin Tinubu Ba? Fadar Shugaban Kasa Ta Yi Martani

  • Shugaban ma'aikatan fadar shugaban kasa Femi Gbajabiamila ya shiga cikin kunshi wadanda ake zargi a badakalar kudi da ake tuhumar dakatacciyar Ministar jin kai Betta Edu
  • Hakan ya samo asali da yadda aka ga wata takardar amincewa da sakin kudi Naira Biliyan 3, ga ma'aikatar ta, wadda yanzu haka ke ci gaba da zagaya kafafen sada zumunta
  • Takardar amincewa da diban kudin, ta fara sanya ayar tambaya a zukatan yan kasa, tare da tantanmar anya kuwa da sanin shugaban kasa wajen amince domin fitar da kudin

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Aisha Musa ta shafe tsawon shekaru tana kawo labaran Hausa a bangaren siyasa, tsegumi da al’amuran yau da kullum

Abuja - Mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin labarai, Bayo Onanuga, ya yi martani kan wata takarda da aka fitar na cewa an amince da Naira biliyan 3 don tantance rajistar shirye-shirye da aka samar a zamanin gwamnatin Buhari.

Kara karanta wannan

Tinubu, Shettima da gwamnoni sun dira Ibadan don taya Akande murnar cika shekera 85

Kamar yadda Business day ta rahoto, an yi zargin cewa takardar wacce ta yadu a shafukan sada zumunta, ta fito ne daga hannun shugaban ma’aikatan fadar gwamnatin tarayya, Femi Gbajabiamila.

Fadar shugaban kasa ta magantu kan zargin kasancewar Gbajabiamila a badakalar Edu
Betta: Gbajabiamila Ya Amince da N2bn Ba Tare da Izinin Tinubu Ba? Fadar Shugaban Kasa Ta Yi Martani Hoto: Bola Ahmed Tinubu/Dr Betta Edu/Femi Gbajabiamila
Asali: Facebook

Haka kuma, an yi zargin cewa takardar ta nuna cewa Shugaban kasa Tinubu ya umurci dakatacciyar ministar harkokin jin kai, Dr Betta Edu, da ta saki naira biliyan 3 domin tantance rijistar shirin.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sai dai kuma, ana zargin cewa Gbajabiamila ya amince da kudin ne ba tare da izinin Tinubu ba.

Betta Edu: Tarin badakaloli a ma'aikatar jin kai

Sabbin zarge-zargen na zuwa ne yayin da hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta EFCC ke tsaka da binciken badakala a ma'aikatar jin kan.

Tun farko dai an samar da rijistan ne don shirye-shiryen bayar da tallafi ga marasa karfi.

Kara karanta wannan

Bwala: Hadimin Atiku ya faɗi abu 1 da zai yi idan Shugaba Tinubu ya naɗa shi muƙami a gwamnati

An yi zargin cewa kamfanoni da dama sun samu kwangila daga naira biliyan 3 din da aka bai wa dakatacciyar ministar, lamarin da ya haddasa cece-kuce tare da sa shugaban kasar bayar da izinin bincike a kai.

N3bn don tantance rijista: Bayo Onanuga ya yi martani

Da yake martani kan ci gaban a ranar Litinin, 15 ga watan Janairu, Onanuga ya bukaci yan Najeriya da daure sannan su kara hakuri, yana mai gargadi kan hukuncin kafafen yada labarai.

Sai dai kuma, sabanin zargin da ake yi, Onanuga ya tabbatar da cewar Shugaba Tinubu ya amince da sakin naira biliyan 3 don tantance rijistan, rahoton Punch.

Jaridar Punch ta nakalto Onanuga na cewa:

"Shugaban kasar ya umurci EFCC da ta binciki ma'aikatar jin kai da duk wadannan batutuwa da tuni suke karkashin binciki."
“Ina da tabbacin cewa EFCC ta rigada ta ga wannan takarda daga ofishin shugaban ma’aikatan shugaban kasa kuma suna yin wani abu a kan wadannan bincike.

Kara karanta wannan

Bayan nasara a Kotun Koli, Gwamna Abba Gida-Gida ya ba Kwankwaso, Ganduje da Gawuna mukamai

“Mu kyalesu su yi aikinsu. Kada mu kasance masu yin bincike sau biyu a kan magana daya, ko kuma a yi shari'ar kafofin watsa labarai kan batun da ake bincike. ‘Yan Najeriya su yi hakuri.
"Da zaran EFCC sun kammala bincikensu, za su gabatar da rahotonsu ga shugaban kasar wanda zai dauki mataki kan sakamakon binciken."

Aisha Musa ta shafe tsawon shekaru tana kawo labaran Hausa a bangaren siyasa, tsegumi da al’amuran yau da kullum

Malamin addini ya yi hasashen tsige Gbajabimala

A wani labari na daban, Legit Hausa ta kawo a baya cewa Shugaban cocin INRI Evangelical Spiritual, Primate Elijah Ayodele, ya gargadi Femi Gbajabiamila, shugaban ma'aikatan shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, da ya zama mai sa ido sosai.

A wani sakon gargadi da ya saki a shafinsa na X (wanda aka fi sani da Twitter a baya) a ranar Alhamis, 28 ga watan Disamba, Primate Ayodele ya bayyana cewa ya gargadi na hannun damar shugaban kasar a baya.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng