Hotuna Sun Kayatar Yadda Sunusi Lamido Ya Jagoranci Sallar Juma'a a Legas, Bayanai Sun Fito

Hotuna Sun Kayatar Yadda Sunusi Lamido Ya Jagoranci Sallar Juma'a a Legas, Bayanai Sun Fito

  • An yada hotunan tsohon Sarkin Kano, Sunusi Lamido Sunusi a jihar Legas inda ya jagoranci sallar Juma'a
  • Tsohon sarkin ya jagoranci sallar Juma'ar a babban masallacin Sakatariyar jihar a Alausa da ke Legas
  • Rahotanni sun tabbatar da cewa Sarkin ya ziyarci jihar Legas ce don halartar taron tunawa da tsaffin sojojin Najeriya

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Legas - Tsohon Sarkin Kano, Sunusi Lamido Sunusi ya jagoranci sallar Juma'a a jihar Legas.

Tsohon sarkin ya jagoranci sallar Juma'ar a babban masallacin Sakatariyar jihar a Alausa da ke Legas.

Hotunan Sunusi Lamido a masallacin Juma'a a Legas
Hotunan Yadda Sunusi Lamido Ya Jagoranci Sallar Juma'a a Legas. Hoto: @masoyansunusi2.
Asali: Twitter

Mene dalilin Sunusi Lamido na zuwa Legas?

Lamido ya halarci masallacin ne yayin bikin tuna wa da ranar tsaffin sojojin Najeriya a jihar Legas, cewar Daily Trust.

Kara karanta wannan

Fitaccen dan Majalisa ya shiga takarar neman gwamna a jihar PDP, ya caccaki gwamna mai ci

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sunusi wanda ya rike mukamin gwamnan Babban Bankin Najeriya, CBN a mulkin tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan.

Lamido ya yi kaurin suna wurin fadar gaskiya komai dacinta a duk lokacin da ya ga ana wani abin da bai kamata ba a kasar.

Wane lamari Sunusi ya fi tsoma baki a Najeriya?

Mai Martaban ya fi tsoma baki mafi yawan lokuta a abubuwan da suka shafi tattalin arzikin Najeriya da sauran wurare da suka shafi rayuwar al'umma.

A kwanakin baya ya yi magana kan cire tallafin mai wanda tun a farkon mulkin tsohon shugaban kasa, Jonathan ya nemi a cire tallafin.

Daga bisani shugaban ya yi yunkurin cire tallafin amma ya fuskanci zanga-zanga a dukkan fadin kasar baki daya kan lamarin.

Har ila yau, hawan Bola Tinubu ke da wuya ya tabbatar da cewa ya cire tallafin man fetur a ranar 29 ga watan Mayu.

Kara karanta wannan

Shehu Sani ya yi shagube ga Betta kan alkawarinta na fitar da yan Najeriya miliyan 50 daga talauci

Sunusi ya fadi babbar hanyar magance matsalar fetur

A wani labarin, tsohon Sarkin Kano, Sunusi Lamido Sunusi ya bayyana hanyar dakile tsadar man fetur a Najeriya.

Sunusi ya ce rage dogaro da man fetur ce hanya kadai da zai kawo sauki wa 'yan Najeriya kuma ya karya farashin.

Tsohon Sarkin ya bayyana haka ne a ranar 19 ga watan Oktoba yayin gabatar da wata lakca a jihar Legas.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.