Kwanaki Kadan Bayan Samun Matsala a Afirka, Dangote Ya Sake Sabon Matsayi, Ya Ci Kazamar Riba

Kwanaki Kadan Bayan Samun Matsala a Afirka, Dangote Ya Sake Sabon Matsayi, Ya Ci Kazamar Riba

  • Alhaji Aliko Dangote ya sake karbe matsayinsa a matsayin wanda ya fi kowa kudi a Nahiyar Afirka baki daya
  • Dangote ya samu karuwar kudi har dala biliyan 10 a ranar 8 ga watan Janairu idan aka kwatanta da dala biliyan 9.5 a wancan makon
  • Wannan na zuwa ne makwanni kadan bayan attajirin ya rasa matakinsa na wanda ya fi kowa arziki a Nahiyar

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

FCT, Abuja - Shahararren dan kasuwa a Najeriya, Aliko Dangote ya sake komawa matsayinsa na wanda ya fi kowa kudi a Nahiyar Afirka.

Wannan na zuwa ne kwanaki kadan bayan attajirin ya rasa matakinsa na wanda ya fi kowa arziki a Nahiyar.

Kara karanta wannan

Sanata Ndume ya maida martani kan dakatar da ministar jin kai, ya aike da sako ga Tinubu

Dangote ya samu kazamar riba a jiya, ya koma matsayinsa na da a Afirka
Dangote ya koma matsayinsa a Afirka bayan samun kazamar riba. Hoto: Johann Rupert, Aliko Dangote.
Asali: Getty Images

Yaushe Dangote ya rasa matsayinsa a Afirka?

Dangote ya rasa matakin nasa bayan dan kasar Afirka ta Kudu, Johann Rupert ya karbe matsayin a wurin attajirin da ke rike da matsayin tun da jimawa.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Kamar yadda rahoton Forbes ta tabbatar, Dangote ya samu karuwar kudi har dala biliyan 10 a ranar 8 ga watan Janairu.

Aliko Dangote ya kwace kujerar daga hannun Rupert wanda ya rike matsayin a kasa da mako daya inda hakan ya jawo cece-kuce a Najeriya.

Nawa Dangote ya mallaka a yanzu a Afirka?

A ranar 8 ga watan Janairu Rupert ya na da akalla dala biliyan 10 idan aka kwatanta da dala biliyan 10.7 a ranar 30 ga watan Janairun 2023.

A halin yanzu, Dangote ya na matakin 191 a duniya yayin da Rupert ke matakin 197 a fadin duniya baki daya.

Kara karanta wannan

Innalillahi: Tsohon Atoni-janar a jihar Arewa ya riga mu gidan gaskiya da shekaru 81

Attajirin Najeriya ya ci gaba da rike matsayin wanda ya fi kowa kudi a Afirka da dala biliyan 15.5, cewar rahoton Bloomberg.

Dangote ya rasa matsayinsa a Nahiyar Afirka

A wani labarin, Attajirin dan kasuwa, Alhaji Aliko Dangote ya rasa matakin kasancewa wanda ya fi kowa kudi a Afrika.

Johann Rupert shi ya karbe matsayin da ribar dala biliyan 10.3 idan aka kwatanta da na Dangote da ke da dala biliyan 9.5.

A yanzu attajirin ya karbe matsayinsa na wanda ya fi kowa arziki a Nahiyar ta Afirka gaba daya.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.