Gwamnonin Arewa Ta Tsakiya Sun Fadi Abu 1 da FG Za ta Yi Kan Hare-Haren Plateau

Gwamnonin Arewa Ta Tsakiya Sun Fadi Abu 1 da FG Za ta Yi Kan Hare-Haren Plateau

  • Gwamnonin jihohin Arewa ta Tsakiya sun kai ziyarar ta'aziyya kan mutanen da suka rasa ransu a jihar Plateau
  • Gwamnonnin sun yi kira da gwamnatin tarayya da ta gano tushen rikicin domin samar da dauwamammen zaman lafiya
  • A yayin ziyarar gwamnonin sun kuma bayar da gudunmawar N100m mutanen da haren-haren suka ritsa da su

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Jihar Plateau - Ƙungiyar gwamnonin Arewa ta Tsakiya (NCGF) ta buƙaci gwamnatin tarayya ta gano tushen kashe-kashen da ake yi a jihar Plateau domin samun dawwamammen zaman lafiya.

Gwamnonin Arewa ta Tsakiya sun ziyarci Plateau
Gwamnonin Arewa Ta Tsakiya sun bayar da tallafin N100m kan mutanen da harin Plateau ya ritsa da su Hoto: Caleb Mutfwang
Asali: Twitter

Jaridar Daily Trust ta ce Shugaban ƙungiyar, Gwamna Abdullahi Sule na jihar Nasarawa, ya yi wannan kiran a Jos, a ranar Talata lokacin da ya jagoranci takwarorinsa a ziyarar ta’aziyya ga gwamnan jihar Plateau, Caleb Mutfwang.

Kara karanta wannan

Gwamna Fubara ya bayyana dalili 1 da yasa ya amince da yin sulhu a rikicinsa da Wike

A hare-haren da aka kai a jajibirin Kirsimeti a wasu ƙauyuka 23 na ƙananan hukumomin Bokkos, Mangu, da Barkin Ladi, an salwantar da rayukan sama da mutum 150.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sule ya bayyana hare-haren a matsayin ta’addanci tsantsa, sannan ya buƙaci a samar da na’urori na zamani domin gano masu aikata laifuka tare da daƙile ayyukansu a yankin Arewa ta tsakiya.

Wane kira gwamnnonin suka yi?

Gwamnan na Nasarawa ya ƙara da cewa an dade ana kai hare-haren kuma ya dage cewa dole ne masu ruwa da tsaki daban-daban su gano tushen matsalar tare da samar da dawwamammiyar mafita a gare ta.

A cewarsa:

"Ranka ya dade, mun zo ne domin neman da ka jajirce wajen gano tushen wannan lamari domin ba za mu iya cigaba da rayuwa a haka ba."

Baya ga kokarin da ake yi a matakin jiha, shugaban gwamnonin na Arewa ta Tsakiya ya kuma yi kira ga gwamnatin tarayya da ta gano tushen kashe-kashen da ake ta fama da shi.

Kara karanta wannan

Bayan ya samu babbar matsala, gwamnan PDP ya yi magana kan hakura da mukaminsa

Ya ce ta haka ne kawai za a iya samo bakin zaren warware rikicin da ya shafe sama da shekaru ashirin ana fama da shi.

A cewarsa:

“Mun ga irin wannan yanayi a Rwanda domin ba zan kira abin da ke faruwa a Plateau rikicin manoma da makiyaya ba, domin ba shi ba ne."

Jaridar The Nation ta kuma rahoto cewa a yayin ziyarar, gwamnonin sun ba waɗanda hare-haren suka ritsa da su gudunmawar N100m.

Shugaba Tinubu Ya Ɗau Zafi Kan Harin Plateau

A wani labarin kuma, kun ji cewa shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu, ya yi Allah wadai da hare-haren da aka kai a jihar Plateau.

Shugaban ƙasar ya umarci jami'an tsaro da su gaggauta shiga cikin dajin domin zaƙulo miyagun da suka kai hare-haren.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng